An yi canjaras tsakanin Algeria da Burkina Faso a Gasar AFCON

Yanzu dai Burkina Faso da Angola ne a saman teburin rukunin D kowanne da maki hudu-hudu.

An yi canjaras tsakanin Algeria da Burkina Faso a Gasar AFCON

Bayan ana tashi wasan Burkina Faso da Algeria

Algeria da Burkina Faso sun tashi da canjaras 2-2 a wasan da suka barje gumi a Gasar Kofin Nahiyar Afirka ta AFCON da gudana a Ivory Coast.

Dan wasan Burkina Faso, Mohamed Konate ne ya fara zura kwallo a ragar Algeria gab da za a tafi hutun rabin lokaci a fafatawar da aka yi a filin wasa na Stade de Bouake.

Sai dai bayan an dawo daga hutun rabin lokaci ne dan wasan Algeria Baghdad Bounedjah ya farke kwallon a minti na 51.

A cikin minti na 70 ne kuma Burkina Faso ta sake samun wata damar, inda dan wasanta Bertrand Traore ya zura kwallo ta biyu a ragar Algeria ta hanyar bugun fenariti.

Sai dai murnar ‘yan wasan Burkina Faso ta koma ciki bayan da Bounedjah ya zura kwallo ta biyu a ragarsu.

Yanzu dai Burkina Faso da Angola ne a saman teburin rukunin D kowanne da maki hudu-hudu, inda ita kuma Algeria ke biye da su da maki biyu, sai Mauritaniya wadda Angola ta lallasa da 2-3 a kasan tebur babu maki ko daya.

An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

‘A sansanin gudun hijira na yi sakandare har na zama likita’

An dawo da wutar lantarki a Kaduna

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja