An yi ruwan kankara zalla a Taraba

Kankarar ce zalla ta rika sauka, babu ruwa

An yi ruwan kankara zalla a Taraba

An yi ruwan kankara zalla a garin Nguroje da ke karamar hukumar Sardauna a tsaunin Mambilla na Jihar Taraba.

An yi ruwan ne a ranar Talata kuma an kwashe kimanin awa daya ana yin shi ba tare da saukan ruwa irin wanda aka saba gani ba.

Wani mazaunin garin na Nguroje mai suna Abdulrashid Jobbdi ya shaida wa Aminiya cewa wannan lamari ya bai wa mazauna garin mamaki.

A cewarsa, ba su taba samun ruwan na kankara zalla ba, sai dai akan sami saukar kankara a lokacin ruwan sama.

“Amma yau a maimakon ruwan sama, sai kankara zalla ta sauka,” a cewar Abdulrashid.

Zaɓen Edo: Duk wanda ya kaɗa ƙuri’a ya koma gida ya zauna — ’Yan sanda

Hotunan yadda Zaɓen Gwamnan Edo ke gudana

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo