An yi wa ma’aikata karin albashi a Anambra

Gwamnan ya yi wa ma’aikata kyautar dubu 15 don yin bikin Kirsimeti.

An yi wa ma’aikata karin albashi a Anambra

Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo

Gwamnan Anambra, Charles Soludo, ya yi wa ma’aikatan gwamnatin jihar karin kashi 10 na albashi, wanda zai fara aiki a watan Janairun 2023.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ma’aikatan gwamnati na 2022 a dakin taro na Jerome Udoji da ke Awka.

Kazalika, Soludo ya ba da umarnin bai wa ma’aikatan kyautar N15,000 don gudanar bikin Kirsimeti a jihar.

Ya sake jadadda aniyarsa na ci gaba da yakar bata gari a lungu da sako ja jihar.

Anambra dai na fama da hare-haren ’yan awaren Biyafara (IPOB), wadanda sukan sanya dokar zaman gida.

Amma gwamnan ya ce zai ci gaba da yaki da IPOB har ya kawo karshensu.