Ana gudanar da zabuka lafiya a rumfunan Yobe
A safiyar yau Asabar ana gudanar zabukan ‘yan takarar Gwamna da ‘yan majalisu a duk rumfunan zaben jihar Yobe, an fara cikin zaman lafiya yayin da jama’a da dama suka fito don kada kuri’arsu a duk sassan jihar. Wakilinmu ya ziyarci rumfanan zaben Damaturu babban birnin jihar inda ya ce, an fara tantance masu kada […]
A safiyar yau Asabar ana gudanar zabukan ‘yan takarar Gwamna da ‘yan majalisu a duk rumfunan zaben jihar Yobe, an fara cikin zaman lafiya yayin da jama’a da dama suka fito don kada kuri’arsu a duk sassan jihar.
Wakilinmu ya ziyarci rumfanan zaben Damaturu babban birnin jihar inda ya ce, an fara tantance masu kada kuri’a da misalin karfe 8 na safe a mafi yawan rumfunan zaben.
Rahotan na bayyana cewa, an girke jami’an tsaro a duk rumfunan zaben.