APC ta lashe duk kujerun kananan hukumomi a zaben Sakkwato

APC ta lashe duk kujerun ciyamoni da kansiloli a zaben kananan hukumomin Jihar Sakkwato.

APC ta lashe duk kujerun kananan hukumomi a zaben Sakkwato

APC

Jam’iar APC ta lashe duk kujerun zaben shugabannin kananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar a Jihar Sakkwato.

Shugaban Hukumar Zaben Jihar Sakkwato, Aliyu Suleiman, ya sanar a ranar Litinin cewa APC ta yi nasara a daukacin kananan hukumomi 23 da ke fadin jihar, kamar yadda hukumar zaben jihar.

A cewarsa, ’yan takarar APC ne suka lashe zaben kananan hukumomi 23 da kujerun kansiloli da ke fadin jihar, a zaben da jam’iyyu 15 suka fafata.

Bayan sanar da sakamakon zaben hukumar ta mika wa zababben jagororin kananan hukumomin takardar shaidar cin zabe.

Da La’asar din Litinin din nan ake sa ran rantsar da sabbin shugabannin kananan hukumomin.