AU ta zama mamba ta dindindin a kungiyar kasashen G-20

India ta nemi a bai wa Tarayyar Afirka gurbi na dindindin na zama mamba a kungiyar G-20.

AU ta zama mamba ta dindindin a kungiyar kasashen G-20

Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta zama sabuwar mamba a kungiyar kasashen G-20 masu karfin tattalin arziki ranar Asabar bayan Firaiministan India Narendra Modi ya gayyace ta.

Fadada kungiyar babbar nasara ce ta fannin diflomasiyya ga Modi, wanda zai sake fafatawa a zaben kasar a shekara mai zuwa kuma ya yi amfani da damar karbar bakuncin taron wajen kara wa kansa kima a idanun duniya.

Kafin ya bude taron, Modi ya gaishe da shugaban Tarayyar Afirka kuma shugaban kasar Comoros Azali Assoumani inda ya rungume shi.

“India ta nemi a bai wa Tarayyar Afirka gurbi na dindindin na zama mamba a kungiyar G-20.

“Na yi amannar cewa kowa ya amince da hakan,” a cewar Modi a jawabinsa ga mahalarta taron.

“Ina kira ga shugaban Tarayyar Afirka ya zo ya zauna a kujerarsa ta dindindin a G-20 bayan amincewar kowa da kowa,” in ji shi, inda ya doka sandar da ke hannunsa wacce ke nuna an yarda da matakin.

Daga nan ne Assoumani ya je ya zauna a wurin da shugabannin kungiyar suka zauna bayan Ministan Harkokin Wajen, India S. Jaishankar ya yi masa iso.

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi

NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi tan 3.9 da kama mutum 599

An kashe ’yan gudun hijira uku a Sakkwato

Kotu ta soke hukuncin yi wa Jam’iyyar NDC rijista