Ba za mu sake tallafa wa Buhari ba- Gali Na’Abba
Tsohon Shugaban Majalisar Wakilai na tarayya, Gali Umar Na’Abba ya ce shi da wasu masu ra’ayi irin nasa ba za su tallafawa Shugaba Buhari ba wajen fafutukar neman zaben badi. Gali Na’Abba wanda yana daya daga cikin kwamitin Amintattu na Jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a wani zantawa da ya yi da wakilin kafar […]

Tsohon Shugaban Majalisar Wakilai na tarayya, Gali Umar Na’Abba ya ce shi da wasu masu ra’ayi irin nasa ba za su tallafawa Shugaba Buhari ba wajen fafutukar neman zaben badi.
Gali Na’Abba wanda yana daya daga cikin kwamitin Amintattu na Jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a wani zantawa da ya yi da wakilin kafar sadarwa ta The Cable.
A cewarsa, “Mutane da yawa sun taimaka masa wajen yakin neman zabe, sannan suka zabe shi. Na bar Jam’iyyar PDP ne domin in goya masa baya, saboda na yi tunanin zai kawo wani sauyi ga dimukradiyya.
“Yanzu shekara uku ke nan da fara mulki. Bai aiki da ‘yan jam’iyya, yana kallon ‘yan jam’iyyar a matsayin mutanen banza,” in ji shi.