Ba zamu kori manyan jami’an tsaro yanzu ba: Fadar Shugaban kasa
Fadar shugaban kasa ta mayar da martani akan kiraye-kirayen da ake ta yi wa shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, na ya kori manyan jami’an tsaron kasa duba da tabarbarewar al’amuran tsaro a kasar, fadar shugaban kasar ta bayyana cewa ba zata kori manyan jami’an tsaron ba a daidai wannan lokacin. Sakataren Gwamnatin tarayyar Najeriya Boss Mustafa, […]
Manyan jami’an tsaron Najeriya
Fadar shugaban kasa ta mayar da martani akan kiraye-kirayen da ake ta yi wa shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, na ya kori manyan jami’an tsaron kasa duba da tabarbarewar al’amuran tsaro a kasar, fadar shugaban kasar ta bayyana cewa ba zata kori manyan jami’an tsaron ba a daidai wannan lokacin.
Sakataren Gwamnatin tarayyar Najeriya Boss Mustafa, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a sa’ilin da ya halarci taron kaddamar da littafi a birnin tarayya Abuja.
Ya ce, ba a korar manyan jami’an tsaron haka kawai, “Akwai matakan da ake bi wajen yin hakan, kana na tabbata idan lokaci ya yi za abi matakan, ba za a wayi gari lokaci guda a kori manyan jami’an ba.” In ji shi.
Ya kamata Buhari ya kori manyan jami’an tsaron kasa – Kadariya Ahmed