Ba zan ce uffan kan rikicin NNPP a Kano ba — Kwankwaso

Jagoran na NNPP ya ce ba shi da abin da zai ce game da rikicin.

Ba zan ce uffan kan rikicin NNPP a Kano ba — Kwankwaso

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran ɗariƙar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ba zai yi magana kan rikicin cikin gida da ke faruwa a jam’iyyar a Jihar Kano.

Da ’yan jarida suka tambaye shi game da rikicin a gidansa da ke Miller road a Kano, a ranar Talata, Kwankwaso ya ce ba shi da abin cewa.

“Ba na son yin magana game da batun. Don Allah kada ku sanya ni cikin abin da ba na da alaƙa da shi. Shugaban jam’iyya ya riga ya yi magana, kuma yana ci gaba da magana a kai, ku tuntuɓe shi,” in ji shi.

Aminiya ta ruwaito yadda rikicin cikin gida ya sanya shugaban jam’iyyar NNPP na Kano, ya dakatar da Sakataren Gwamnatin Jihar, Abdullahi Baffa Bichi da Kwamishinan Sufuri, Muhammad Diggol.

Shugaban jam’iyyar, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya bayyana cewa an dakatar da su ne saboda zargin rashin girmamawa jam’iyyar.

Kazalika, ya ce sun yi amfani da muƙamansu ba bisa ƙa’ida ba, da rashin biyayya ga jam’iyyar.

Dakatarwar ta biyo bayan wani yunƙurin da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi na sasanta sakataren gwamnatin da ‘yan mazaɓarsa da suka samu matsala.

Haka kuma, sakataren ya nesanta kansa daga wata ƙungiya da ke neman raba Gwamna Yusuf da Kwankwaso, wanda ta ke yi wa gwamnan taken “Abba, ka tsaya da ƙafarka.”

Abba ya yi tafiya yayin da rikici ya dabaibaye NNPP a Kano

Kotu ta hana EFCC kama tsohon minista kan taƙaddamar fili

Isra’ila ta ɗaiɗaita yara sama da 400,000 a Lebanon — UNICEF

Ba zan ce uffan kan rikicin NNPP a Kano ba — Kwankwaso