Balogun na shirin canza sheka

dan kwallon Najeriya Leon Balogun da yake buga wa kulob din Sb Darmstadt da ke Jamus ya bayyana cewa ba zai sabunta kwantaraginsa a kulob din ba. Kulob din Darmstadt dai ya samu hayewa rukunin gasar rukunin Bundesliga ta Jamus ne a kakar wasa ta bana amma duk da haka Balogun ya ce ba shi […]

Balogun na shirin canza sheka
Balogun na shirin canza sheka

dan kwallon Najeriya Leon Balogun da yake buga wa kulob din Sb Darmstadt da ke Jamus ya bayyana cewa ba zai sabunta kwantaraginsa a kulob din ba.

Kulob din Darmstadt dai ya samu hayewa rukunin gasar rukunin Bundesliga ta Jamus ne a kakar wasa ta bana amma duk da haka Balogun ya ce ba shi da niyyar sabunta kwantaraginsa a kulob din.
Balogun, wanda ya buga wa Najeriya Super Eagles wasa sau hudu kawo yanzu, yana daga cikin ’yan kwallon da suka buga wa kungiyar Super Eagles kwallo da Chadi a ranar Asabar da ta gabata a Kaduna.
Sai dai rahotanni sun ce akwai yiwuwar Balogun ya cigaba da yin kwallo Jamus a wani kulob bayan ya bar kulob din Sb Damstadt.

Sojoji sun daƙile harin Boko Haram, sun ceto mutum 9 a Borno

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 3 a Binuwai

Mahara sun sace bsarake, sun harbi matarsa a ƙauyen Ondo

Sarkin Musulmi ya umarci a fara neman jinjirin watan Muharram