Barazanar Boko Haram: Ba zan mayar da martani ba yanzu- Pantami

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Intanet, Dokta Isa Ali Pantami, ya shaida cewa zuwa yan zu ba zai ce ko mai ba game da barazanar da jagoran wani bangare na  kungiyar Boko Haram Abubakar Shekaru ya yi masa ba. Shaikh Pantami, ya bayyana haka ne a sa’ilin da yake gabatar da mukala akan fasahar zamani […]

Barazanar Boko Haram: Ba zan mayar da martani ba yanzu- Pantami

Isa Ali Pantami, Ministan Sadarwan Najeriya. (Tsohuwar ajiya).

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Intanet, Dokta Isa Ali Pantami, ya shaida cewa zuwa yan zu ba zai ce ko mai ba game da barazanar da jagoran wani bangare na  kungiyar Boko Haram Abubakar Shekaru ya yi masa ba.

Shaikh Pantami, ya bayyana haka ne a sa’ilin da yake gabatar da mukala akan fasahar zamani a makarantar sakandare ta Garki da ke birnin tarayya Abuja. Inda yake amsa tambayoyin manema labarai sai ya ce, “Babu abin da zance kan wannan barazanar a yanzu.”

Ministan na yin rangadi a makarantun sakandaren ne, inda yake yi wa dalibai lakcoci kasancewar da dama daga cikin su na fuskantar karancin wadanda zasu basu shawarwari akan fannin ilimin fasahar sadarwa da irin tasirin fannin ga tattalin arzikin kasa na zamani.

‘Yan ta’adda na amfani da shafukan zumunta don samun mambobi – Pantami

 

A-Kurkura: Guba ko Magani?

Tsohon Shugaban Jami’ar Ilori, Farfesa Ambali ya rasu

ICPC ta hana El-Rufai ganin likita —Hadiminsa

Hanyoyin zuwa Katsina sun zama tarkon mutuwa