Barazanar yajin aiki: Akwai wadatar man fetur- NNPC
Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, akwai wadataccen man fetur a Najeriya da zai isa masu hulda da man a fadin kasar duk da barazanar yajin aikin da kungiyar kwadago take yi. Kamfanin NNPC ya tabbatar da hakan ne, kamar yadda kakakin kamfanin Mista Ndu Ughamadu ya sanar. Ughamadu […]
Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, akwai wadataccen man fetur a Najeriya da zai isa masu hulda da man a fadin kasar duk da barazanar yajin aikin da kungiyar kwadago take yi.
Kamfanin NNPC ya tabbatar da hakan ne, kamar yadda kakakin kamfanin Mista Ndu Ughamadu ya sanar.
Ughamadu ya ce, kamfanin nada wadataccen mai da zai kai na kwana 39 ana amfani da shi da kuma karin na kwana 25 da aka ajiye.