Bare United za ta ci gaba da fafatawa duk da rashin shiga Rukuni na Daya na ’Yan dagaji
Kungiyar kwallon kafa ta Bare United da ke garin Billiri a Jihar Gombe za ta ci gaba da fafatawa a wasa don ganin ta cimma burinta duk da ba ta samu hayewa Rukunin na 1 na ajin ’yan dagaji na kasa. Sakataren Kungiyar Umar Billiri ya karin ce wannan rashin nasara da ba su samu […]
Kungiyar kwallon kafa ta Bare United da ke garin Billiri a Jihar Gombe za ta ci gaba da fafatawa a wasa don ganin ta cimma burinta duk da ba ta samu hayewa Rukunin na 1 na ajin ’yan dagaji na kasa.
Sakataren Kungiyar Umar Billiri ya karin ce wannan rashin nasara da ba su samu hayewa ba a wannan karo ba abu ne da zai sanyaya musu gwiwa ba. “Mun yi bakin kokarinmu a yanzu amma za mu koma mu sake duba kura-kuranmu sannan mu shirya a nan gaba,” inji shi.
Umar ya yi kira ga masu hannu da shuni da kuma mahukuntan Karamar Hukumar Billiri su taimaka Wa kungiyar da tallafin kudi domin a halin yanzu kusan mutum daya ne yake daukar nauyinta.
“Muna kira ga mahukuntan Karamar Hukumar Billiri su tallafa wa wannan kungiya da kudi, domin a halin yanzu Shugaban Kungiyar Alhaji Alhassan Galadima ne kadai yake daukar dawainiyarta,” inji shi.