Batun matar da take auren maza biyu ya canja salo
karar da Kabir Mohammed Jibiya ya shigar inda yake neman Hindatu Yusuf da ta fito masa da mijin da ta ce matarsa Amina Kabir take da shi a Katsina tare kuma zarginta da bata mata suna a kotun Shari’a da ke Jibiya da Mai shari’a Alhaji Kabir Hamisu Bello ya fara saurare tun a ranar […]
karar da Kabir Mohammed Jibiya ya shigar inda yake neman Hindatu Yusuf da ta fito masa da mijin da ta ce matarsa Amina Kabir take da shi a Katsina tare kuma zarginta da bata mata suna a kotun Shari’a da ke Jibiya da Mai shari’a Alhaji Kabir Hamisu Bello ya fara saurare tun a ranar 3/5/2016 ya dauki sabon salo.
A wancan zaman dai har wadda ake kara Hindatu Yusuf ta fara gabatar wa kotu da shaidun kariya a kan furucin da ta yi na cewa,”mijin Amina da ke Katsina,” wanda aka dage cigaba da sauraren wannan kara har zuwa 9/5/2016 amma zaman da bai yiwu ba a wannan rana saboda dalilai na tsaro, wanda hakan ya sanya alkali ya sake bayar da wata ranar domin cigaba da sauraren shari’ar,amma sai aka maido shari’ar a wata kotun a cikin garin Katsina kafin zuwan waccan rana da aka sanya. Ba a dai samu damar cigaba da sauraren wannan shari’a da aka kawo ba a wannan kotu da ke Katsina saboda sake mayar da ita waccan kotu da ke Jibiya, wadda ita ce ta fara sauraren karar domin ta cigaba da ita.
Kotun shari’ar da ke garin Jibiya wadda Mai shari’a Alhaji Kabir Hamisu Bello ke jagoranta ta cigaba da sauraren wannan kara wadda Kabir Mohammed Jibiya ya shigar inda yake neman Hindatu Yusuf da ta fito masa da miji na biyu da ta ce matarsa Amina Kabir na da shi a Katsina, a yayin da ita Hindatun ta yi wannan furuci a wata karar da ta shigar, inda take neman Amina da ta biya kudin da take binta bashi wadda ta ce tayi amfani da kudin inda ta bai wa mijinta na Katsina ya cika ya sayi mota. Wancan furucin da Hindatu ta yi ne, wanda ya fado a cikin kunnen Kabir wanda yake cikin kotu a lokacin da ake sauraren karar da ita Hindatu ta shigar, ya ba Kabir damar shigar da kara a kan ita Hindatun.
Kamar yadda Aminiya ta jiyo daga wata majiya da ke da kusanci da kotun (da ta nemi a boye suna),ta shaida mana cewa,bayan an kai wannan shari’a a Katsina a lokacin da aka ce an sake maido ta a wancan kotun ta Jibiya,shi Kabir ya rubuta takardar janye wannan kara da ya shigar amma kotu ta ki amincewa da haka har sai an tattaro duk wadanda shari’ar ta shafa, wadanda kuma suka hadu a ranar 6/6/2016 domin cigaba da sauraren shari’ar, wadda aka zauna a dakin alkali(chamber)saboda matakan tsaro.
Da kotu ta juya kan Kabir mai kara don jin ko yana da sauran wata alaka da Amina? Kabir ya amsa da cewa, “yanzu babu sauran wata alaka tsanina da Amina, saboda na ba ta takarda tun ranar 17/1/2015.” Har’ila yau,alkali ya tambaye shi ko wancan auren da tayi halak ne? Ya amsa da cewa, na halak ne. Da alkali ya tambaye shi cewa,to me ya sa ya yi mamakin maganar Hindatu? Sai ya amsa da cewa, “saboda ban sani ba,ba ta sanar da ni ba.” Amma kuma ya shaida wa kotu cewa,wannan saki da ya yi na biyu ne,kuma ta zauna a gidansa ne bayan ya sake ta, saboda tana dauke da ciki wanda shi ne ya bata damar ta zauna don ta yi idda, wanda yayi zaton ko sun shirya. Har wayau,alkali Kabir ya tambayi Kabir, ko shi ne waliyin Amina,kuma yanzu ya ga sabon mijin? Kabir dai ya amsa cewa ba shi ne waliyin Amina ba kuma ya ga sabon mijin da ya nemi Hindatu da ta kawo masa. A lokacin da kotu ta nemi jin cewa,ya san ya ba matarsa takarda tsawon shekara guda cewa ta yi wani auren? Sai Kabir ya amsa da cewa, “saboda ba ta fada mani ta yi aure ba, kuma tana zaune a gidana”.
Mai karar dai ya ce ya shigar da kara ne duk da bai yi bincike ba, saboda ita Amina ba ta gaya masa ta yi auren ba. Ya ce ya yi jayayyane a kan maganar Hindatu ne da farko,amma yanzu ya yi bincike ya kuma gano gaskiyar magana. Da alkali ya tambaye shi cewa,haka zasu cigaba, tana Katsina tana gidansa? Sai Kabir ya ce,wannan zabin