Bayan kai masa hari, Gwamna Ortom ya yi ganawar sirri Buhari
A ranar Talata Gwamna Samuel Ortom na Jihar Binuwe, ya yi wata ganawar sirri da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta da ke Abuja. Ganawar na zuwa ne kwanaki kadan da wasu ’yan bindiga suka kai wa gwamnan hari a karshen makon da ya gabata. Mayakan Boko Haram sun kashe mutum uku a Kamaru […]
Gwamna Ortom tare da Shugaba Buhari
A ranar Talata Gwamna Samuel Ortom na Jihar Binuwe, ya yi wata ganawar sirri da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta da ke Abuja.
Ganawar na zuwa ne kwanaki kadan da wasu ’yan bindiga suka kai wa gwamnan hari a karshen makon da ya gabata.
A ranar Asabar ce ’yan bindiga suka kai wa ayarin motocin gwamnan hari yayin da yake dawowa daga gonarsa a kauyen Tyomu da ke kan babbar hanyar Makurdi zuwa Gboko.
Bangarori da dama a kasar sun yi ta Allah wadai da harin, inda Shugaban Kasar a ranar Lahadi ya bai wa hukumomin tsaro umarnin gudanar da bincike mai zurfi a kan lamarin.