Boko Haram: Buhari zai yi taro da shugabannin yankin Tafkin Chadi yau

Shugaban Najeriya Muhammadu zai yi wani taro don ganawa da shugabannin kasashen yankin tafkin Chadi su shida a yau Alhamsi, a cikin shugabannin harda shugaban kasar Chadi Idriss Deby wanda za a yi a N’Djamena babban birnin Chadi kan batun Boko Haram. Shugaba Buhari ne zai jagoranci taron a matsayinsa na shugaban gwamnatin kasashen yankin […]

Boko Haram: Buhari zai yi taro da shugabannin yankin Tafkin Chadi yau

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu zai yi wani taro don ganawa da shugabannin kasashen yankin tafkin Chadi su shida a yau Alhamsi, a cikin shugabannin harda shugaban kasar Chadi Idriss Deby wanda za a yi a N’Djamena babban birnin Chadi kan batun Boko Haram.

Shugaba Buhari ne zai jagoranci taron a matsayinsa na shugaban gwamnatin kasashen yankin tafkin Chadi, kamar yadda mai taimaka wa Shugaban akan watsa labarai Femi Adesina ya sanar.

Ana saran taron zai sake duba batun yanayin tsaro a yankunan da rikicin Boko Haram ke shafa, da kuma inganta Rundunar Hadin Gwiwa ta kasa da kasa don ceto yankin daga halin da yake ciki.