Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Rahotanni sun ce maharan sun kuma yi ƙoƙarin ƙwace sansanin sojoji da ke yankin.

Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Wasu mayakan Boko Haram

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari ƙauyen Logomani da ke Ƙaramar Hukumar Ngala a Jihar Borno, inda suka ƙone wani ofishin ’yan sanda da cibiyar kula da lafiya.

Rahotanni sun ce maharan sun kuma yi ƙoƙarin ƙwace sansanin sojoji da ke yankin.

Mukaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Operation Hadin Kai, Kyaftin Muhammed Goni, ya ce sojoji sun daƙile harin tare da fatattakar maharan.

Sai dai ya ce soja guda ya rasu, yayin da motocin yaƙi guda biyu da wasu kayan aikin rundunar suka lalace.

Ya ce, maharan sun samu shiga wani ɓangare na sansanin yayin artabu, amma sojojin sun sake tsara kansu tare da mayar da martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa bayan sun yi asara.

Goni ya kuma ce sojojin Bataliya ta 115 sun ceto mutum biyu da aka yi garkuwa da su a Askira/Uba, tare da ƙwato Naira miliyan 1.2 da kayan abinci da sauran kayayyakin da ake zargin ana amfani da su wajen tallafa wa ayyukan ’yan ta’adda.

Ma’aikatan Abuja ba sa sona — Wike

Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Mutane Biyu Sun Mutu, Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Ruwan Sama A Gashuwa

Gwamnati ta ƙara albashin sojoji — Ministan Tsaro