Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Wata majiya ta ce sun shiga gida-gida suna harbi suna neman kayan abinci.

Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum

’Yan Ta’addan Boko Haram sun kai hari ƙauyen Kaleri da ke Ƙaramar Hukumar Jere a Jihar Borno, inda suka sace mutum biyu da kayan abinci masu tarin yawa.

Wata majiya daga yankin ta tabbatar da cewa lamarin ya faru ne kusa d Jami’ar Maiduguri (UNIMAID).

Majiyar ta ce, “Sun shigo da manyan makamai, suna harbe-harbe suna bi gida-gida don neman kayan abinci, suna sanya tsoro a zukatan mazauna garin.”

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Sun yi garkuwa da mutane biyu, sannan suka kwashe kayan abinci.”

Bayan faruwar lamarin, jami’an ’yan sanda sun rufe yankin tare da kama wasu mutane, amma ba su bayyana cewar waɗanda suka kama na da alaƙa da harin ba.

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas

Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje

Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba