Boko Haram ta kai sabon hari a garin Geidam

Mayakan Boko Haram sun kai sabon hari dab da bude-baki a garin Geidam ranar Juma’a.

Boko Haram ta kai sabon hari a garin Geidam

Mayakan ISWAP
(Tsohuwar ajiya).

Mayakan Boko Haram sun kai sabon hari a garin Geidam na Jihar Yobe, da Magaribar ranar Juma’a.

Mayakan a cikin motoci dauke da muggan makamai sun yi wa garin dirar mikiya ne tun da misalin karfe shida na yamma.

Mazauna garin sun shaida wa Aminiya ta wayar salula cewa, “Da shigan maharan garin, sai ayarin motocinsu ya zarce zuwa makarantar firamaren da ke Kafela suka fara barin wuta babu kakkautawa.

“A halin yanzu muna cikin gidajenmu muna addu’ar Allah Ya kare mu; Iya abin da zan iya cewa ke nan a yanzu.”

Kakakin ’yan sandan Jihar Yobe, Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da harin, tare da cewa tuni dakarun sojin sama suka isa garin domin kai dauki.

Sai dai ya ce babu karin bayani game da yawan mutanen da lamarin ya ritsa da su, a halin yanzu.

Na ƙi biyan kuɗin fansar ’yan uwana sun kuɓuta — Gwamnan Zamfara

Ma’aikatan Abuja ba sa sona — Wike

Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Gwamnati ta ƙara albashin sojoji — Ministan Tsaro