Boko Haram Ta Kwace Yankunan Borno ta Arewa —Shugaban Majalisa
Shugaban majalisar ya ce Boko Haram na rike da wasu yankunan kananan hukumomin jihar guda biyu
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdulkarim Lawan, ya ce a halin yanzu, Boko Haram na rike da ikon yankunan kananan hukumomi biyu a jihar.
Abdulkarim Lawan ya nuna damuwarsa kan dawowar ayyukan Boko Haram, duk da cewa Gwamnatin Tarayya ta dage cewa babu wani yanki a jihar da ya rage a hannun ’yan ta’addar.
- NAJERIYA A YAU: ’Yan Bindiga Sun Zafafa Hare-Hare Bayan Samuwar Mai A Bauchi
- ’Yan bindiga sun kashe ’yan kasuwa 4 a Katsina
Shugaban majalisar ya ce a halin da ake ciki, yankunan kananan hukumomin Guzamala da Kukawa a yankin Borno ta Arewa suna karkashin ikon ’yan ta’addar ne.
Lawan wanda shi ne wakilin Guzamala a Majalisar Dokokin jihar, ya yi wadannan banyan ga manema labarai ne a ranar Lahadi.
Ya yi kira ga sojoji da su kara himma tare da kwato yankunan da lamarin ya shafa daga Boko Haram don maido da zaman lafiya a cikinsu.