Bom ya kashe almajirai 4 da wasu 2 a Borno
Abun fashewan ya tashi ne a cikin wani kango da ke kusa da tsangayar almajiran
Yadda tashin bom ya yi wata tawa mota. (Tsohon hoto).
Wani abun fashewa ya kashe wasu kananan yara almajirai hudu da wasu manya biyu a Karamar Hukumar Gubio a Jihar Borno.
Shugaban karamar hukumar, Mali Gubio, ya ce abun fashewan ya tashi ne a cikin wani kango da ke kusa da tsangayar almajiran a safiyar ranar Asabar.
“ِAn gano gawar kananan yara almajirai hudu da wasu manya biyu, amma har yanzu ba a kai ga gano ’yan uwansu ba
“Dukkansu sun rasu, saboda baka ba za mu iya fadin hakikanin abin da ya faru ba, amma dai abun fashewa ya tashi a wani gida da ake ajiye kayan gwangwan,” in ji s hugaban karamar hukumar.
- An yanke mazakutar malamin allo daf da aurensa a Zariya
- An kama matar da ta sayar da kananan yara 42
A cewarsa, wasu na zargin ’yan bola-jarin sun dauko abun fashewan bisa rashin sani ne suka hada da kayan da suka tara a kangon da ke kusa da tsangayar.
Shugaban karamar hukumar ya kuma jaddada umarnin Gwamna Babagana Umara Zulum, na haramta ayyukan ’yan bola-jari a jihar, da nufin hana sace-sace kayan gwamnati a wuraren da mutane suka kaurace wa.