Buhari da Atiku za su sanya hannu akan amincewar sakamakon zabe
Shugaba Muhammadu Buhari na jam`iyyar (APC) da tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar dan takarar jam`iyyar adawa ta PDP za su sanya hannu akan amincewar sakamakon zaben takarar shugaban kasa da za a yi ranar 16 ga Fabirairu. A makon nan ne tsohon shugaban Amurka Bill Clinton zai gana da Shugaba Buhari da Atiku don […]
Shugaba Muhammadu Buhari na jam`iyyar (APC) da tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar dan takarar jam`iyyar adawa ta PDP za su sanya hannu akan amincewar sakamakon zaben takarar shugaban kasa da za a yi ranar 16 ga Fabirairu.
A makon nan ne tsohon shugaban Amurka Bill Clinton zai gana da Shugaba Buhari da Atiku don samun gudanar zabe cikin zaman lafiya, kamar yadda kakakin tsohon shugaban Angel Ureña ya sanar.
Kwamitin zaman lafiya na kasa wanda tsohon shugaban Najeriya Abdulsalami Abubakar ke jagoranta suka sanar da hakan.