Buhari ya dage gabatar da takararsa zuwa ranar Laraba
Tsohon Shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari ya dage gabatar da niyyarsa ta tsaywa takarar Shugaban kasa daga shekaranniya Laraba zuwa Laraba mai zuwa 15 ga Oktoba. Kafar labarai ta NEWSWIRE NGR, ruwatito cewa sanarwa dagewar tana kunshe ne cikin wata takarda dauke da sanya hannun Ko’odinetan Kwamitin Kamfe na Buhari ne Dokta Audu Ogbeh. Sai dai […]
Tsohon Shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari ya dage gabatar da niyyarsa ta tsaywa takarar Shugaban kasa daga shekaranniya Laraba zuwa Laraba mai zuwa 15 ga Oktoba. Kafar labarai ta NEWSWIRE NGR, ruwatito cewa sanarwa dagewar tana kunshe ne cikin wata takarda dauke da sanya hannun Ko’odinetan Kwamitin Kamfe na Buhari ne Dokta Audu Ogbeh.
Sai dai sanarwar ba ta bayyana wani dalili na dage gabatarwar ba, sai dai ta ce: “Niyyar gabatarwar da aka shirya yi a ranar Laraba (shekaranjiya) 8 ga Oktoba, 2014 yanzu ta koma ranar Laraba 15 ga Oktoba, 2014 a dandalin Eagle Skuare da ke Abuja.”