Buhari ya isa Makurdi don yakin neman zabe
A yau Laraba Shugaba Muhammadu Buhari ya isa Makurdi babban birnin jihar Benuwai don gudanar da yakin neman zabensa a karo na biyu. Buhari ya sauka a jihar ne tare da jigogin jam`iyyar APC da wasu Gwamnoni. Ana saran shugaba zai ziyarci fadar sarkin tibi wato Tor Tiv, Farfesa James Ayatse, yayin da zai gana […]
A yau Laraba Shugaba Muhammadu Buhari ya isa Makurdi babban birnin jihar Benuwai don gudanar da yakin neman zabensa a karo na biyu.
Buhari ya sauka a jihar ne tare da jigogin jam`iyyar APC da wasu Gwamnoni.
Ana saran shugaba zai ziyarci fadar sarkin tibi wato Tor Tiv, Farfesa James Ayatse, yayin da zai gana da Gwamnan jihar B
enuwai Samuel Ortom kafin ya isa filin wasa na Aper Aku don yin kamfen dinsa.