Buhari ya kara wa manyan hafsoshin tsaro wa’adi
Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari ya amince da karin wa’adin manyan hafsoshin tsaron kasar da suka hada da Babban Hafsan Tsaro, Babban Hafsan Sojin Qasa, Babban Hafsan Sojan Sama, da Babban Hafsan Sajan Ruwa. Tuni dai wannan ta samu sa hannun Ministan Tsaro, Mansur Dan-Ali, wanda jami’in yada labaransa, Kanar Tukur Gusau ya sanar da manema […]
Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari ya amince da karin wa’adin manyan hafsoshin tsaron kasar da suka hada da Babban Hafsan Tsaro, Babban Hafsan Sojin Qasa, Babban Hafsan Sojan Sama, da Babban Hafsan Sajan Ruwa.
Tuni dai wannan ta samu sa hannun Ministan Tsaro, Mansur Dan-Ali, wanda jami’in yada labaransa, Kanar Tukur Gusau ya sanar da manema labarai a yau Litinin a ofishinsa, wanda ya bayyana umarni tare da amincewar shugaban kasa, sannan kuma ya jinjinawa shugabannin tsaron bisa namijin kokarin da suka nuna a yayin ceto kasar daga rigingimun ta’addanci da sauran matsalolin tsaro da kasar ke fuskanta a baya.