Buhari ya rantsar da Alkalin Alkalan Najeriya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a yau Laraba ya rantsar da Ibrahim Tanko Mohammed a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya CJN. Tun a watan Janairu 2019 Ibrahim yake rike da mukamin Mukaddashin Alkalin Alkalan Najeriya, bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalan Najeriya CJN Walter Onnoghen daga mukamin.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a yau Laraba ya rantsar da Ibrahim Tanko Mohammed a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya CJN.
Tun a watan Janairu 2019 Ibrahim yake rike da mukamin Mukaddashin Alkalin Alkalan Najeriya, bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalan Najeriya CJN Walter Onnoghen daga mukamin.
