Jonathan jajirtaccen mutum ne, inji Buhari

Shugaba Buhari ya yaba kyawawan dabi’un Jonathan a matsayin Shugaba da kuma wakili

Jonathan jajirtaccen mutum ne, inji Buhari

Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a lokacin wata ziyara da ya kai wa Shugaba Muhammadu Buhari a Fadar Shugaban Kasa

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yaba da jajircewar Tsohon Shugaba Goodluck Jonathan da kuma yadda ya jawo wa Najeriya martaba da kima a idon duniya.

Shugaban ya bayyana hakan ne a sakon taya murnar cika shekara 63 a duniya da ya aike wa Mista Jonathan din.

“Shugaba Buhari ya jinjina daukaka mai ban mamaki wadda ba kasafai akan ga irinta ba a fagen siyasar Najeriya da tsohon shugaban kasar ya samu, da kuma jajircewarsa wadda ta ba shi damar aiki a baya-bayan nan a matsayin manzon kungiyar ECOWAS na musamman wajen dawo da zaman lafiya a Jamhuriyar Mali”, inji sakon mai dauke da sa-hannun Hadimin Shugaban Kasa kan Watsa Labarai, Femi Adesina.

A ranar Juma’a ne Mista Jonathan, wanda Buhari ya gada a mulki a 2015. ke cika she 63 da haihuwa.

Ya yi addu’a Allah Ya ba wa tsohon shugaban karin hikima, da lafiya da tsawon kwana mai albarka domin ci gaba da hidimta wa al’umma.

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa

Masu zanga-zanga sun tare babbar hanyar Abuja kan matsalar tsaro

Janar Rabe Abubakar ya rasu a hannun ’yan bindiga