Coronavirus ta kashe karin mutum 7 a Najeriya, 838 sun kamu

Alkaluman Hukumar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa a Najeriya NCDC, sun nuna cewa an samu karin mutum 838 da cutar Coronavirus ta harba ranar Lahadi a fadin kasar. Cikin bayanan da hukumar ta wallafa a shafinta na yanar gizo kamar yadda ta saba duk rana sun nuna an kuma samu karin mutum bakwai da suka mutu […]

Coronavirus ta kashe karin mutum 7 a Najeriya, 838 sun kamu

Wani Jami’in kiwon lafiya daga cikin gidan gilashi yana daukar samfuri daga jikin wata mata da ake yiwa gwajin coronavirus a jihar Ogun

Alkaluman Hukumar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa a Najeriya NCDC, sun nuna cewa an samu karin mutum 838 da cutar Coronavirus ta harba ranar Lahadi a fadin kasar.

Cikin bayanan da hukumar ta wallafa a shafinta na yanar gizo kamar yadda ta saba duk rana sun nuna an kuma samu karin mutum bakwai da suka mutu sakamakon cutar a fadin Najeriya.

Sabbin alkaluman da suka nuna an samu karin mutum 838 da suka harbu sun fito ne daga jihohi 16 da suka hada da; Abuja (297), Legas (253), Filato (82), Kaduna (57), Katsina (32), Nasarawa (31) da Kano (25).

Sauran su ne; Gombe (24), Oyo (8), Ribas (8), Zamfara (7), Ogun (4), Bauchi (4), Edo (4), Anambra (1) da kuma Sakkwato (1).

Da wannan adadi, jimillar mutum 84,414 sun harbu da cutar a Najeriya, yayin da kuma mutum 1,254 suka riga mu gidan gaskiya.

Ya zuwa yanzu dai an salami mutum 71,034 daga cibiyoyin killace masu dauke da cutar bayan sun samu waraka.

 

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta