COVID-19: Jihar Osun na raba shinkafa buhu 40,332 ga mabukata
Ta fitar da tsari don tabbatar da rabon ya kai ga kowane bangare
Gwamnatin Osun ta fara rabon buhunan shinkafa dubu arba’in da 333 ga jama’ar jihar domin saukaka musu radadin annobar COVID-19.
Wadanda za su samu tallafin sun hada da marasa galiyu, nakasassu, tsofaffin ma’aikata, malaman addinin Musulunci da na Kirista, da kuma maza da mata.
- An gano mai dauke da Coronavirus da ta gudu a jihar Osun
- An ba wadanda suka saci kayan tallafin Osun sa’o’i 72 su dawo da su
Shugaban Kwamitin Sanya Ido a kan rabon tallafin, Mista Ademola Adebisi, a ranar Alhamis, ya ce Gwamnatin Jihar ta yi tsari da yadda kowane bangare a jihar zai ci moriyar tallafin.
Ya kara da nuna farin cikinsa na ganin yadda rabon kayan tallafin ke tafiya bisa tsari.
A cewarsa tsarin da aka bi wajen rabon kayan tallafin zai tabbatar da cewar kowane bangare ko yanki na jihar ya samu na rabonsa.