COVID-19: Saudiyya ta dakatar da ’yan kasashe 20 shiga kasarta

Ta hana baki daga Amurka, Ingila da Daurlar Larabawa da sauransu shigar ta saboda COVID-19.

COVID-19: Saudiyya ta dakatar da ’yan kasashe 20 shiga kasarta

Saudiyya ta dakatar da mutane daga wasu kasashe 20 shiga kasarta, a sabon yunkurinta na hana yaduwar cutar COVID-19 a karo na biyu.

Sanarwar daga Ma’aikatar Harkokin Cikin Gidan Saudiyya ta ce umarnin Masarautar zai fara aiki ne daga ranar Laraba da dare.

“Matakin da aka dauka kan kasashe 20 din ya biyo bayan umarnin da Masarautar ta bayar.

“Duk dan kasar Saudiyya da ya fito daga kasashen zai shigo Saudiyya ne bisa matakan kariyar COVID-19,” inji sanarwar.

Rahotanni sun bayyana cewa jerin kasashen da Saudiyya ta dakatar din su ne: Amurka, Ingila, Jamus, Faransa, Turkiyya, Japan, Indiya, Pakistan, da Sweden.

Sauran su ne: Ajantina, Daular Larabawa, Indonisiya, Ireland, Brazil, Portugal, Afrika ta Kudu, Switzerland, Lebanon, Masar.

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa