Cutar ƙyandar biri ba ta ɓulla a Gombe ba – Gwamna Inuwa

Gwamnan ya ce jihar ta shirya ko da cutar za ta ɓulla.

Cutar ƙyandar biri ba ta ɓulla a Gombe ba – Gwamna Inuwa

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayyana cewar ba a samu rahoton ɓullar cutar ƙyandar biri a jihar ba.

Amma, ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa, gwamnatinsa ta shirya tsaf don tunkarar cutar tare da daƙile ta.

Ya yaba wa Cibiyar Daƙile Cututtuka ta Ƙasa (NCDC) bisa ɗaukar matakan da suka dace don hana yaɗuwar cutar.

Gwamnan, ya kuma jaddada cewa NCDC tare da haɗin gwiwar hukumomin lafiya na jihohi suna sanya ido sosau kan cututtuka a jihar tare da ɗaukar matakan da suka dace.

Ya bayyana cewa yana da yaƙinin cewa jihohin sun shirya tunkarar ɓarkewar cutar, tarw da haɗin gwiwar NCDC.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labaran gwamnatin jihar, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, ya Gombe na da cibiyoyin gwaje-gwaje da ɗakunan bincike guda huɗu da ke jiran ko-ta-kwana.

A ranar Lahadi ne, NCDC ta ayyana ɓarkewar cutar ƙyandar biri a faɗin Najeriya.

Cibiyar ta ce yanzu haka akwai mutum 39 da suka kamu da cutar, kuma jihohin Bayelsa, Kuros Riba, da Jihar Legas na gaba wajen wuraren da aka fi samun masu kamuwa da cutar.