Cutar Ebola: Hukumomin Alhazai sun dauki mataki
A sakamakon bullar cutar Ebola a wani yanki na kasar nan, cikin maniyyata aikin hajjin bana ya duri ruwa, musamman da suka ji cewa kasar Saudiyya ta hana maniyyatan kasashen Saliyo da Guinea da kuma Liberiya da cutar ta yi kamari zuwa aikin hajji da umura har sai abin da hali ya yi.Hukumomin kasar Saudiyya […]

A sakamakon bullar cutar Ebola a wani yanki na kasar nan, cikin maniyyata aikin hajjin bana ya duri ruwa, musamman da suka ji cewa kasar Saudiyya ta hana maniyyatan kasashen Saliyo da Guinea da kuma Liberiya da cutar ta yi kamari zuwa aikin hajji da umura har sai abin da hali ya yi.
Hukumomin kasar Saudiyya dai sun ce saboda bullar cutar duk wani maniyyaci da zai shiga kasarsu sai an tabbatar da koshin lafiyarsa kafin a bar shi ya shiga kasar.
Sai dai kuma hukumomi a Najeriya ba su yi kasa a gwiwa ba wajen ganin cutar ba ta bazu wadansu yankunan na kasar nan ba, inda suka himmatu wajen ganin cewa cutar ta takaita ne a Legas kawai, watau wurin da Mista Patrick Sawyer da ya shigo da cutar daga kasar Liberiya ya sauka.
Hukumar alhazai ta kasa da sauran hukumomin alhazai na jihohi sun bayyana cewa sun dauki kwararan matakai domin ganin cutar ba ta shafi wani maniyyaci daga kasar nan ba.
A cewar Uba Mana, kakakin hukumar alhazai ta kasa, hukumar tasu ta umarci hukumomin alhazai da ke jihohin kasar nan su tabbatar sun tantance kowane maniyyaci a yayin da ya isa sansanin alhazai kafin ya tashi zuwa kasa mai tsarki. Yana mai gargadin cewa ba za a bar duk wanda aka ga yana da alamar cutar a tare da shi ya fita kasar nan ba, kuma idan aka samu wani alhaji ya kamu da cutar a kasa mai tsarki ba za a bar shi ya dawo gida ba, sai ya warke.
Shi ma Kwamishinan Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), mai kula da shiyyar Arewa maso Yamma, Alhaji Salisu Ado Shinkafi, ya bayyana shirin da hukumar jin dadin Alhazai ta kasa take yi dangane da cutar Ebola, inda ya ce, “Hukumar NAHCON tana iyakar kokarinta wajen ganin ta fadakar da maniyyata irin matakan da aka dauka domin kare su daga wannan cutar.
“Za mu cigaba da fadakar da su har zuwa lokacin tashi a kullum yadda za su kare kansu. Wadannan ka’idoji da jami’an asibiti suka fadi ne za a cigaba da fada wa jama’a, domin mu ba masana ba ne a fannin aikin kiwon lafiya. Amma idan an fadi mana mu fada, za mu yi kokari mu fada domin cigaban al’ummarmu,” inji shi.
Daga Jihar Sakkwato kuma wakilinmu Nasiru Bello ya ruwaito Alhaji Faruku Umar, mai taimaka wa hukumar jin dadin alhazai ta jihar kan harkokin yada labarai kuma sakataren karamin kwamitin wayar da kan alhazai yana cewa, “Hukumarmu ta jin dadin alhazai, karkashin jagorancin Alhaji Muntari Mai gona ta dauki duk wani matakin da ya dace domin wayar da kan maniyyatan Jihar Sakkwato domin su kare kansu daga kamuwa da wannan cutar ta Ebola. A yau da kake magana da ni mun fara zagaye a kananan hukumominmu 23 don wayar da kansu domin su san mene ne wannnan kwayar cutar; me ke kawo ta; ya mutum zai yi ya kare kansa daga kamuwa da wannan cutar? Da sauran bayanai da suka shafi kiwon lafiya.”
Ya kara da cewa, “Ka san wannan cutar har yanzu ba ta zo gefenmu ba, amma duk da haka a kowace karamar hukuma da muka je tare da jami’an lafiya muke zuwa domin yin gwaji ga kowane Alhaji da Hajiya don tantance su, da zarar muka samu mai wata babbar matsalar ciwo, kamar tari ko juna biyu da sauransu, za mu hana shi zuwa tare da maye gurbinsa.”
Alhaji Faruku, wanda ya yi wa wakilinmu wannan bayanin ta waya, ya ci gaba da cewa, “Yanzu haka hukumar ta samo na’urar gwaji da ake amfani da ita domin tantace masu wannan cutar, wadda za su yi aiki da ita, babu wani maniyyaci a Jihar Sakkwato da zai shiga jirgi sai mun tantance lafiyarsa, duk wanda muka samu da wani zazzabi da aka kasa ganewa, za mu hana shi shiga jirgi, har sai ma’aikatan lafiya sun yi binciken kwakwaf a kansa. Da haka nake son fada maka cewa duk wani shiri na samun nasara muna aiwatar da shi ga maniyyatanmu, za mu kuma cigaba da yi har lokacin da aka kammala aikin hajji muka dawo gida Najeriya. Mun dauki matakin da ya kamata ga mahajjatanmu kan cutar Ebola.”
Daga Kaduna kuma wakilinmu Muhammad Yaba, ya ruwaito cewa, Hukumar Jin dadin Alhazai na jihar ta shirya tsaf dangane da kula da lafiyar alhazanta tun daga nan gida zuwa kasa mai tsarki.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Malam Yunusa Muhammad Abdullahi ne ya bayyana haka, inda ya yi nuni da cewa, kamar kowace shekara, hukumar tana mayar da hankali sosai kan batun kiwon lafiyar alhazan jihar, don haka a wannan shekarar ma ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen ba su takardu domin su je asibitin gwamnati a duba lafiyarsu tun kafin a soma tashi zuwa kasar Saudiyya.
“Tuni muka bai wa dukkan alhazanmu fom domin su je asibiti a duba lafiyarsu, watau (tes), tun kafin a fara tashi zuwa Saudiyya. Mata kuma dole sai an duba su ko suna da juna biyu, da dai makamantarsu,” inji shi.
Har ila yau Malam Yunusa ya bayyana cewa, kafin a kammala tantance kowane Alhaji ko Hajiya, sai ta sake yin wani gwaji a sansanin Alhazai, “Duk muna yin hakan ne domin tabbatar da lafiyarsu.”
Haka kuma wata jami’ar lafiya a Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna, Hajiya Zainab Umar ta bayyana a wajen wani taron masu ruwa da tsaki a harkar aikin hajji da aka yi a Hukumar Jin Dadin Alhazan jihar, a makon jiya, cewa gwamnatin jihar tana sane da kalubale da cutar Ebola ke neman janyo wa kasar nan, saboda haka tuni ma’aikatar lafiya da yardar gwamnatin jihar ta samar da sashe na musamman domin kebe duk wani Alhaji ko Hajiya da za a samu da alamun cutar Ebola a filin jirgin sama.
A cewarta, gwamnati ta damu da bullar cutar a Jihar Legas, duk kuwa da cewa ba a samu bullar cutar a Jihar Kaduna ba.
Daga Jihar Legas kuwa, inda cutar Ebola ta bulla a kasar nan, wakilinmu Abubakar Ibrahim ya ruwaito cewa, Hukumar Alhazai ta jihar ta ce a halin yanzu ba ta da wani shiri na musammam game da cutar Ebola ga alhazanta, sai wanda gwamnatin tarayya ta tsara, za ta yi wani abu ne kawai idan tsarin gwamnatin tarayya bai kai ga tasarin da take jin ya dace ba.
Mai magana da yawun hukumar alhazai na jihar, Mista Durojaye ya ce kodayake wannan batu ne na ma’aikar kiwon lafiya, su nasu isar da umurni ne, amma dai a halin yanzu babu wani tsari ko shiri da za a ce an yi da ya bambanta da na sauran jihohi.
Ya ce amma da zarar ma’aikatar kiwon lafiya ta jihar ta fidda wani tsari ko kuma umurni, su kuma hukumar alhazai ba su da zabi. Ya ce sun kammala nasu shirin game da gudanar da aikin hajji na wannan shekarar, ba wani abu da ya rage.
A Jihar Neja kuwa wakilinmu Muhammad danladi Ibrahim ya ruwaito cewa, Sakataren Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai na Jihar Neja, Sheikh Musa Ibrahim ya ce sun dauki matakan da suka hada da wayar wa maniyyata kai ta kafafen watsa labarai da suke fadin jihar.
Sakataren ya ce hukumarsu tana da kwararrun likitocin da ke wayar wa maniyyata kai duk shekara, musamman wadanda za su tashi ta Jihar Neja, game da hanyoyin da ake bi domin kamuwa da cuta, don haka wannan ba sabon abu ba ne a gare su.
Ya ce akwai cibiyoyin tantance jama’a da gwamnatin jihar ta bude guda uku a dukkan shiyyoyin Majalisar Dattawa domin auna wadanda aka gansu da alamun wannan cutar, da suka hada da zazzabi mai tsanani da amai da gudawa, sai zubar jini ta baki da kunnuwa da hanci. Ya ce wadanda suka fi saurin kamuwa da cutar sun hada da masu cin beraye da birai da jemage da alade.
Sai ya shawarci jama’a da su gaggauta zuwa wurin likita a duk lokacin suka ji alamun zazzabi mai tsanani a jikinsu. Ya ce daukar wannan matakin zai taimaka wurin gano hanyoyin da za a yi saurin shawo kan lamarin. Kuma ya kamata su rungumi akidar tsaftace jiki da muhalli kamar yadda Annabi Muhammad [S.A.W.] ya koyar.
A Jihar Yobe kuma wakilinmu Sani Gazas Chinade ya ruwaito cewa Sakataren hukumar alhazai na jihar, Alhaji Bukar Kime ya bayyana cewa hukumarsu tuni ta dauki matakin ilmantar da maniyyatan jihar dangane da cutar Ebola.
Sakataren ya ce sun dauko kwararren likita don ilmantar da maniyyatan dangane da alamomi da kuma illar cutar ta Ebola. Kuma za su cigaba da daukar wannan matakin nasu har sai sun ga komai ya yi daidai.
Daga Kano kuma, jihar da ta fi yawan maniyyata a Najeriya, wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Sakataren hukumar alhazan jihar, amma aka ce ya yi tafiya, shi kuma Jami’in hulda da jama’a ya ce ba zai ce komi ba dangane da batun cutar Ebola, sai dai ma’aikatar lafiya. Da wakilinmu ya nufi ma’aikatar lafiyar, bai yi sa’ar samun wani bayani ba.
A waje daya kuma, daya daga cikin likitocin nan da suka kamu da cutar ta Ebola, sakamakon yi wa dan kasar Liberiyan nan magani ta rasu cikin dare ranar Talata a birnin Ikko a inda aka kebe su ana yi musu magani.
Likitan, mai suna Ameyo Stella Adedayo, tana sahun farko cikin likitocin da suka duba Mista Patrick Sawyer, a wani asibiti mai zaman kansa da ke unguwar Obalende a cikin birnin Ikko. Bayanai sun nuna cewa ita dai wannan baiwar Allah da ta rasu, tana da sama da shekaru 55, tana cikin manyan likitocin asibitin da aka kai Mista Sawyer jinya. Kuma a lokacin da aka kai Mista Sawyer asibitin ba ta aiki, tana gida aka kira ta domin ta taimaka wajen ceto ran majinyacin, ashe shi ne zai zama sanadiyyar rasuwarta.
A halin yanzu dai adadin wadanda suka mutu sakamakon wannan cutar sun kai biyar ke nan a Najeriya, a yayin da kuma mutane biyar suka warke, inda likitoci suka tabbatar ba su dauke da kwayar cutar.