Cutar Ebola ta zama alakakai

Cutar Ebola ta zama alakakai ga wadansu kasashe da ke yankin Afirka ta Yamma ciki har da Najeriya sakamakon yadda aka fara mayar da su saniyar ware a tsakankanin kasashen  duniya.Ministan lafiya  Farfesa Onyenbuchi Chukwu kuma ya bayyana cewa gwamnati ta ayyana dokar ta-baci a kan cutar, domin haka wata cibiyar daukar matakan gaggawa na […]

Cutar Ebola ta zama alakakai

Cutar Ebola ta zama alakakai ga wadansu kasashe da ke yankin Afirka ta Yamma ciki har da Najeriya sakamakon yadda aka fara mayar da su saniyar ware a tsakankanin kasashen  duniya.
Ministan lafiya  Farfesa Onyenbuchi Chukwu kuma ya bayyana cewa gwamnati ta ayyana dokar ta-baci a kan cutar, domin haka wata cibiyar daukar matakan gaggawa na hana bazuwar cutar ta fara aiki a jihar Legas  daga jiya  Alhamis, ba dare ba rana.
Annobar wadda zuwa yanzu ta hallaka kusan mutum 900, ta sa wadansu kasashen duniya da dama sun fara daukar matakan kiyaye bullarta cikin kasashensu. Wannan ya sa a ranar Talata mahukunta a kasar Ghana suka haramta wa ’yan Najeriya da sauran ’yan kasashen ’yankin izinin shiga kasar. Hakazalika, kasar Saudiyya ta bayyana haramta wa wadansu kasashen yankin Afirka ta yamma uku (Laberiya da Guinea da Saliyo) izinin zuwa aikin Hajjin bana, sakamakon barkewar cutar mai saurin kisa a kasashensu.  
Cutar mai saurin yaduwa ta fara bulla ne kimanin shekara 38 da suka wuce a tsohuwar kasar Zaire, wato Jamhuriyar Dimukradiyyar Kongo a yanzu. Inda daga can ne aka rada mata sunan Ebola, wanda ya samo asali daga sunan wani rafi a garin da cutar ta fara bulla a wancan lokacin. Kodayake a watan Fabrairun bana ne kwayar cutar ta kara bulla, amma wannan karon a kasar Guinea wadda take yankin Yammacin Afirka, inda daga nan ne ta ci gaba da yaduwa zuwa kasashen Saliyo da Laberiya da kuma Najeriya.
Kodayake an tabbatar da cewa kwayar cutar ta shigo kasar  nan ne bayan da wani dan Laberiya, mai suna Patrick Sawyer ya rasu a karshen watan jiya sanadiyyar cutar a wani asibiti da ke unguwar Obalende ta jihar Legas. An yi amannar cewa marigayin ya dauko kwayar cutar ne daga kasar Laberiya bayan wata ziyara da ya kai can, kwana biyar kafin rasuwarsa. Har ila yau, a makon jiya ne mazauna jihar Anambra suka shiga zaman fargabar bullar annobar bayan wadansu rahotonni da ke cewa an shigo da wata gawa jihar daga Laberiya wadda aka yi amannar cutar ce ta yi ajalinta.
A ranar Litinin da ta gabata ne kuma Ministan Kiwon Lafiya Farfesa Onyebuchi Chukwu ya tabbatar da cewa likitar da ta duba Mista Patrick  a jihar Legas, ta kamu da cutar. Ministan  ya ce ana can ana yi mata magani, kuma a yanzu mutane 70 da aka tabbatar cewa sun yi mu’amala da mamacin, ana kula da su, inda takwas daga cikinsu aka kebe su. An kuma dauki jinin karin wadansu mutum uku da alamu suka nuna suna dauke da kwayar cutar, domin yin gwaji.
Sai dai kuma a shekaranjiya laraba minista a ma’aikatar lafiya ya sanar da manema labarai bayan an kammala taron majalisar zartarwaa Abuja cewa wata ma’aikaciyar jinya da ta duba dan kasar Laberiyan ita ma ta rasu, inda ta zama ‘yar Najeriya ta farko da ta rasa ranta a sakamakon cutar, kuma hakan ya sanya aka samu mutane biyu da cutar ta halaka a Najeriya.
A karshen makon jiya ne kuma kamfanin jiragen sama na Emirates ya dakatar da jigila zuwa kasar Guinea har sai abin da hali ya yi saboda annobar. A cikin wata sanarwa a shafinsa na Intanet, kamfanin ya ce ba zai yi sakaci da lafiyar fasinjojinsa da ma’aikatansa ba. Hakazalika wadansu kamfanonin jiragen sama da suka hada da Arik Air da ASky na kasar Togo sun dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa kasashen da cutar ta bulla.
A ci gaba da daukar matakan yaki da bullar cutar, a ranar Litinin ne kasar Koriya ta Kudu ta janye gayyatar da ta yi wa wadansu ’yan Najeriya uku don halartar wani babban taro kan ilimin mata da wata jami’ar kasar ta shirya da hadin gwiwar Majalisar dinkin Duniya.
Ita ma kasar Saudiyya a wani mataki na kandagarki, ta fitar da sunayen kasashe da ba za a ba ’yan kasarsu izinin aikin Hajjin bana ba saboda bullar annobar a kasashen da suka fito. kasashen kuwa su ne Guinea da Saliyo da kuma Laberiya. Hukumomin kasar sun kuma bayyana cewa, dan dasar wanda ya kamu  da cutar  sakamakon ziyarar da kai kasar Saliyo. ya rasu. Kodayake har zuwa wannan lokacin, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ba ta kai ga ba da umarni a hukumance ba kan takaita zirga-zirgar jama’a ko rufe iyakokin kasashen da annobar ta yi kamari ba. Amma hukumar ta ce cikin mutum dubu daya da 603 da aka tabbatar suna dauke da kwayar cutar zuwa yanzu, akwai ’yan Najeriya mutum hudu a ciki.
Ana gane mutumin da ya harbu da cutar ne idan aka ga alamomi kamar su: zazzabi mai tsanani da ciwon gabobin jiki da kasalar jiki da hararwa da kuma gudawa. Har ila yau idan cutar ta ci karfin jiki, tana iya haifar da tsayawar wadansu daga cikin sassan jiki da kuma yoyan jini.
An kama hanyar shawo kan matsalar
Amma duk da cewa da farko masana sun bayyana cewa cutar Ebolar ba ta da rigakafi, ko magani. A yanzu an kama hanyar shawo kanta, inda kwararru a fannin kiwon lafiya suka ce idan aka gane cutar da wuri kuma aka tare ta da magani akwai yuhuwar za a iya samun waraka. Saboda a yanzu haka akwai likitocin Amurka biyu Dokta Kent Brantly da kuma Dokta Nancy Writebol da aka ce sun fara murmurewa daga cutar bayan da suka kamu da ita a lokacin da suke aikin bai wa wadansu da ke dauke da kwayar cutar kulawa a kasar Laberiya.  A karshen makon jiya ne aka koma da likitocin Amurka inda aka nufi wani asibiti da ke birnin Alaska da su. Hakazalika, akwai wani rahoton da ya fito daga kasar Guine da ya ruwaito cewa daya daga cikin likitocin kasar da ke fama da cutar, ya warke.
Bugu da kari akwai kamfanin hada magunguna na Mapp Biopharmaceutical Inc. da ya ce ya kirkiri wani maganin cutar mai suna Zmapp, wanda ya kawo waraka lokacin da aka gwada shi a jikin birrai. Kuma wadansu manasa sun bayyana cewa kwayoyin maganin ne ake ci gaba da gwadawa a jikin likitocin nan na Amurkawa da ke murmurewa daga cutar a halin yanzu.
Wannan ya sa a shekaranjiya Laraba, ministan lafiya Farfesa Chukwu ya kira wani taron manema labarai, inda ya bayyana cewa ma’aikatarsa ta tuntubi Cibiyar Kiyaye Yaduwar Cututtuka ta kasar Amurka don ganin yadd za a samar da maganin a nan Najeriya. Har ila yau, kungiyar likitoci ta kasa wadda membobinta suke cikin yajin aiki, ta bayyana kafa wani kwamiti wanda zai jagoranci yaki da bazuwar cutar da kuma aikin wayarwa da al’umma kai.
Kada a yarda da masu cewa suna da maganinta   -Dokta Sani Gwarzo
Abubakar Ibrahim a Legas

Shugaban yaki  da cutar ebola  Dokta Nasir Sani Gwarzo ya shaida wa   Aminiya cewa  gwamnatocin jihohi  tarayya  sun  hada  hannu  domin  hana  wannan cutar  bazuwa. Ga yadda hirar ta kasance:
Aminiya: Dokta,  da  yake dan kkasar Liberiyan nan da cutar ta kashe  ta  jirgi  ya  shigo  Najeriya,  to su kuma  sauran  wuraren da   ake  shigowa  cikin kasar wadanne  matakai  kuke  dauka  game da su,?
Gwarzo: Mun fara  aiki  a  ire-iren  wadannan bakin iyakokin  da  muke  da ire-iren  su  sun kai  200,  kuma  mun fara  ne  da  manya-manyan tashoshi  da na  sama  da na  ruwa  kuma  har mun kai musu  na’ura da  za su yi  amfani  da ita  na  wuccin-gadi  wanda  daga  nesa  ma  kana  iya  auna  zafin jikin mutum  ba  tare  da ka je  kusa  da shi ko taba shi  ba,  kuma  za mu  kara  karfafa  su,  yanzu  haka  hatta  inda  babu  alamun  wannan cutar  mun  kai  jami’an mu  kuma  har ma  sukan  tsaya  su yi  tambaya  ko da  mai  zazzabi?  sai  a  ware  shi.
Aminiya: Baya  ga mu’amulla  da  mai  wannan cutar,  ta  wace  hanya kuma  ake  kamuwa  da  wannan cutar?
Gwarzo: To  da  farko  dai  wannan  cutar  ta  dabbobi  ce  asalinta,  tana  ciki  jemagu  masu  cin ‘ya’yan  itace, kuma  tana  cikin su  birai,  irin su  gwaggwon biri da barewa  da  gada, ta  cin  wadannan  namun daji  ana  iya  kamuwa,  kuma  ba  cin wadannan  dabbobin ba ne  matsala,  a’a  taba  ruwan  jikin su  ma illa  ne,  wato  a  dauko  naman  wadannan dabbobin a  rike  shi  da  hannu ko  bayan gidansu ko  amansu,  duk  suna  dauke  da  wannan cutar. Amma  yanzu  zancen  da  ake yi  shi ne,  cutar  ta  riga  ta  tsallaka  shinge ta  wuce  cikin  dabbobi  ta  fado kan  jama’a  kuma  ta  fara  yaduwa a  tsakanin dan adam  da  dan adam, shi ne  ya sa  za ka ga  idan mutum  ya  kamu  zai  shafa  wa  wadansu, kuma a irin haka  ne  wani  dan kasar Liberiya  ya zo  ya  shafa wa  likitanmu, shi  ya sa  yanzu  haka  muna  nan muna kula  da  ragowar  ma’aikata, domin an kai  jininsu  a  auna  kuma  da  zaran  an dawo  da  sakamakon Minista  zai yi  bayani  game da  haka.
Aminiya: To beraye  da kyenkyasai  fa, ana  samun wannan cutar  daga  gare  su, ganin su ma  suna  kusa  da  jama’a  sosai?
Gwarzo: A’a, bera  da kyenkyeso  ba su  yadawa,  domin duk karance-karance na  ban ga  inda  aka ce  suna  yada  wannan cutar  ba,  daga  bayyanan  annobar har  yanzu  babu  inda  aka ce suna  yada  wannan cutar,  sai  dai  su din ma  cuta ne,  don haka  a yi kokari  a  guje  musu.
Aminiya: Ganin cewa  likitoci  na  yajin aiki  kuma  gashi  har  yanzu  ana  nan ana binciken, to  yaya  za ku yi  da  wannan kalubalen?
Gwarzo: Ai ba kowa  ne yake yajin aikin ba, akwai  ragowar  ma’aikatan asibiti, kuma  akwai  kilitoci  masu  zaman kansu, kana  akwai  likitocin  da  suka  dawo  suna  bada  gudunmowa   irin ta sa  kai,   hatta  kwamitin  da  muke  aiki  da su  a Legas  akwai likitoci  da  ma’aikatan asibiti  da  suka  kawo  kansu   suka  ce  sun zo ne  domin su bada  gudunmowar su  ga  wannan aikin. Kuma a Abuja yanzu  nake harhada  yadda  za mu  samar  da  wuraren  fadarkawa,  kuma na yi  magana da  wadansu  kwamishinoni da gwamnonin domin daukar  matakan ko- ta-kwana  game da  yaki   da  wannan cutar,  ban tsammanin  cewa  wannan yajin aikin zai yi  tasiri  ga  aikin da muke yi  yanzu.
Aminiya: Yanzu  wane  hali  jihar Legas  take  ciki  game da wannan binciken da  kuke yi?
Gwarzo: Bincike  kam ana nan  ana yi,  domin ko  ba  na kwana  guda ba ne  za a yi  a ce  an tsaya,  ana kan yi,  kuma duk  wanda  aka  bincika  ko da  an ga  bai da  shi  za a jira har bayan kwana  21  kana  za  iya cewa  lallai  bai da  wannan cutar.
Aminiya: An ce wadansu  ‘yan kasar Liberiya sun shigo  Najeriya  domin su ga Fasto T.B.Joshua domin wai ya warkar da su, shin ko kuna sane da wannan ?
Gwarzo: An tura  wakilan gwamnati  sun je  sun yi magana  da shi T. B. Joshua, saboda  ana  tsoron kar  masu  wannan cutar  su  shigo  ya  hada  da su  bai sani ba, ina tabbatar  maka cewa  duk  motar da  za ta  shigo  daga  kasar waje  sai an auna  mutanen,  domin muna  da  na’ura  mai  tantance  masu  zazzabi  wanda  ake  iya  ganin cewa  suna  dauke  da  wannan cutar, sai  dai  idan ta  barauniyar  hanya  ce suka  shigo,  shi  kuma Fasto  mun fada  masa  ya  kula.
Aminiya: Ganin yadda  wannan cutar  ta yo  caa  kan jama’a ko  akwai  wadataccen  maganin ta  ko  kuma  rigakafi?
Gwarzo: Ai ba ma Najeriya  ba,  duk  duniya  ma  har  yanzu  ba a gano  maganinta  ba,  ba a kuma  samo  rigakafinta ba, sai  dai  magunguna  da  za a ba mutum  domin cutar  ta  lafa  jikinsa  ya yi  kwari   kuma kaifinta ya  ragu ainun. Muna  sa  ran  cikin mutane  10  da ke  kamuwa  da  cutar  daga  1-5  suna  rayuwa.
Aminiya: Ke nan  ba a  warke  wannan cutar  kwata-kwata?
Gwarzo: Ana  dai  samun sauki  sosai,  kuma  mutum  zai  samu  kwarin jikinsa.
Aminiya: An ce  wai  namijin goro  na  maganin wannan cutar,  shin da  gaske ne?
Gwarzo: Ni ma  na ji  wannan jita-jitar, a matsayina na ma’aikacin kimiyya  da  kiwon lafiya  ba  zan iya  cewa  da kai  wannan jita-jitar  gaskiya  ne  ba,  illa  iyaka  jita-jita ce,  amma  mutum kar ya yi  amfani  da  jita-jita,  ya yi  amfani  da  abin da  yake  sahihi, kar mutum ya  bata  lokacinsa  wajen cin namijin goro  ya je  ya  bata  cikinsa da  cin  abin da  ba  zai yi  masa  amfani  ba, domin wannan ba  harka  ce ta shaci  fadi  ba.
Aminiya; Wace  shawara  za ka  bai wa  mutane  game  guje wa  kamuwa da  wannan cutar?
Gwarzo: Shawarar da  zan bai wa  mutane  ita ce kada  su  yarda  wannan firgicin ya  ratsa  su  su ki  daukar matakin da ya dace,   mutane  su mike  tsaye su yi  duk  abin da ya dace  wajen ganin sun yi abin da  ya kamata  su yi  game da guje wa  kamuwa  da  wannan cutar, musammam  ta neman sani  game  da  wannan  cutar. Kuma  yanzu  abin da  muka  hango  shi ne,  wadansu  yanzu  haka  sun wasa  wukar su  domin su  cuci  talakawa   game  da  wannan cutar  ta hanyar  cewa  suna  da  maganin cutar, duk wanda  ya ce ya samu  maganin ta  to  ya kawo  dakin bincike  domin a tantance  sahihancin maganin  kafin ya  fara  sayar wa  jama’a