Cutar Kurona: Saudiyya ta hana shiga Makkah da Madina

Kasar Saudiyya ta dakatar da bizar shiga kasar, inda ta sanar da hana maniyatta aikin Hajji da Umrah shiga biranen Makkah da Madina, a wani matakin hana yaduwar cutar Kurona mai alaka da numfashi. A duk shekara miliyoyin mahajjata ne ke shiga biranen Makkah da Madina don sauke farali a kasar. Ma’aikatar harkokin waje ta […]

Cutar Kurona: Saudiyya ta hana shiga Makkah da Madina

Mahajjata suna Sa’ayi tsakanin Safa da Marwa a Saudiyya

Kasar Saudiyya ta dakatar da bizar shiga kasar, inda ta sanar da hana maniyatta aikin Hajji da Umrah shiga biranen Makkah da Madina, a wani matakin hana yaduwar cutar Kurona mai alaka da numfashi.

A duk shekara miliyoyin mahajjata ne ke shiga biranen Makkah da Madina don sauke farali a kasar.

Ma’aikatar harkokin waje ta Saudiyya ta kuma ce za ta hana ‘yan kasashen da aka tabbatar akwai cutar ko tana barazana ga kiwon lafiyar al’umma zuwa kasar.

A cewar mahukuntan kasar Saudiyya sun yi hakan don kaucewar barazar yaduwar cutar da ake kira (COVID-19).