Da gangan jiragen soji suka kai hari Kasuwar Jilli —Minista
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa harin bam da rundunar sojin saman Najeriya ta kai a Kasuwar Jilli, Ƙaramar Hukumar Gubio a Jihar Borno, ba kuskure ba ne.
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa harin bam da rundunar sojin saman Najeriya ta kai a Kasuwar Jilli, Ƙaramar Hukumar Gubio a Jihar Borno, ba kuskure ba ne.
Ta ce yankin an daɗe ana ɗaukar sa a matsayin wurin da ke da hatsari tare da shawarwarin tsaro da suka taƙaita kasancewar fararen hula a wurin.
Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa, inda ya miƙa ta’aziyyar gwamnati ga iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma jajantawa ga waɗanda suka ji rauni.
A ranar 11 ga Afrilu, 2026, rundunar sojin saman Najeriya ƙarƙashin Operation HADIN KAI ta kai hari kan ’yan ta’adda da aka tabbatar suna gudanar da ayyuka a yankin Jilli.
- Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda
- Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe
Ministan ya ce aikin ya biyo bayan dogon leƙen asiri da sa ido kan ayyukan Boko Haram da ISWAP a yankin.
Idris ya bayyana cewa kasuwar Jilli, wadda ake kira “Kasu Daulaye”, ta daɗe tana zama cibiyar ayyukan ta’addanci. A cewarsa, bayanan sirri sun tabbatar da cewa ’yan ta’adda suna amfani da yankin wajen tattara haraji, siyan kayayyaki da tsara hare-hare.
Ya ƙara da cewa a ranar 12 ga Afrilu, sojoji sun kama wani yaro mai shekara 15 da ke aika saƙo ga ISWAP, wanda ya amsa cewa yana kai kuɗi da kayayyaki tsakanin Jilli da sauran wurare.
Ministan ya ce Gwamna Babagana Zulum ya tabbatar masa cewa an rufe kasuwannin Jilli da Gazabure tun shekaru biyar da suka gabata saboda ikon ’yan ta’adda a yankin.
Ya bayyana yankin a matsayin sananniyar cibiyar ayyukan ta’addanci kuma, bayanan sirri sun nuna cewa hanyar Bindul-Jilli ta kasance babbar hanyar da ’yan ta’adda ke amfani da ita.
Ya tuna cewa a watan Janairu sojoji sun sha wahala sakamakon harin bama-bamai a kan hanyar, yayin da hare-haren da aka kai a Ngamdu da Benisheikh a ranar 9 ga Afrilu.
Idris ya ce harin na ranar 11 ga Afrilu ya biyo bayan makonni na sa ido, kuma gwamnati ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa kan harin.
Ya jaddada cewa kare rayukan fararen hula babban wajibi ne ga rundunar soji, tare da tabbatar da ɗaukar alhaki a duk inda ya dace.
Ya ƙara da cewa gwamnati tana aiki tare da gwamnatocin Borno da Yobe, da kuma NEMA da SEMA, don samar da tallafin jin ƙai ga iyalan da abin ya shafa.
Ministan ya buƙaci fararen hula da su kiyaye shawarwarin tsaro, su guji shiga yankunan da aka taƙaita tafiye-tafiye, tare da haɗa kai da hukumomin tsaro.