DAGA LARABA: Ainihin Halin Da Harkar Ilimi Ke Ciki A Jihar Kebbi

Irin halin ni-’yasu da makarantun gwamnati ke ciki a Jihar Kebbi

DAGA LARABA: Ainihin Halin Da Harkar Ilimi Ke Ciki A Jihar Kebbi

Domin sauke shirin latsa nan

Batun lalacewar harkar ilimi a Jihar Kebbi ya dauki hankalin ’yan Najeriya, musamman halin da daliban da ke rubuta jarrabawar sharar fagen shiga jami’a ke ciki.

An jima ana kwarmata batun lalacewar gine-gine da rashin kwararrun malamai da kayan koyarwa a makarantun gwamnatin jihar, wanda hakan ke tarnaki ga samar da ilimi mai inganci.

A wannan karon, shirin Daga Laraba ya yada zango a jihar, inda ya kure wa bangaren ilimin jihar kallo domin gano abin da ya dabaibaye shi da niyyar neman mafita.