DAGA LARABA: Barnar da ’yan bindiga suka yi a Arewa maso Yammacin Najeriya

Shirin namu na yau ya yi nazari kan irin asarar da rikicin ya jawo wa yankin

DAGA LARABA: Barnar da ’yan bindiga suka yi a Arewa maso Yammacin Najeriya

Domin sauke shirin latsa nan

A makon da ya gabata, cikin shirin Daga Laraba, mun kawo muku bayanin asalin ta’addanci a Arewa maso Yammacin Najeriya, inda muka bayyana muku yadda abubuwa suka faro daga Jihar Zamfara.

A wannan karon, shirin ya bankado yawan asarar rayuka da dukiyoyin da aka yi, da kuma yadda zamantakewa ta lalace tsakanin jama’ar wannan yanki sanadiyyar ta’addancin ’yan bindiga.