DAGA LARABA: Yadda Masu Kwacen Waya Ke cin Karensu Babu Babbaka A Kano
Shiri na musamman da ya bi diddigin matsalar, gano masu aikata laifin, abin da ke sa su, da kuma wuraren da aka fi yi a Kano.
Masu kwacen wayar hannu
Domin sauke shirin latsa nan
Kwacen waya ya zama ruwan dare, duk kuwa da cewa idan aka kama mai barawon waya, yana dandana kudarsa.
A halin yanzu, mazauna birnin Kano da dama na cikin mawucyacin hali saboda ayyukan masu kwacen waya, wadanda ke lahanta mutane a bainar jama’a, ba dare, ba rana.
Shirin Daga Laraba na wannan mako, ya yi tattaki zuwa birnin Kano domin bin diddigin matsalar, da kuma gano masu aikata laifin, abin da ke sa su, da kuma wuraren da aka fi yin wannan ta’asa.