Daliban jami’ar Abuja na zanga-zanga kan karin kudin makaranta
Dole ne a janye karin kudin makaranta da aka yi mana.
Wasu daga cikin daliban dauke da kwalaye.
Daliban Jami’ar Abuja sun tare babbar hanyar zuwa filin tashi jirage na Abuja, inda suke gudanar da zanga-zanga kan karin kudin makaranta da jami’ar ta yi.
Kamfanin Dillacin Labarai NAN ya rawaito cewa, an hangi wasu daga cikin daliban yayin da suke zanga-zangar dauke da kwalaye da aka yi rubutu a jikinsu.
- Marayun Abuja sun kubuta daga hannun ’yan bindiga
- Za a rufe kasuwar Wuse da ke Abuja saboda karya dokar COVID-19
- Mutum 994 ne suka rasu a hadura a Abuja a 2020 —FRSC
- Rikicin #EndSARS: Makarantun Abuja na tura dalibai gida
Oladeja Olawale, shugaban Kungiyar Daliban Jami’ar (SUG), ya bayyana cewa sai an biya bukatunsu sannan za su daina zanga-zangar.
Ya kara da cewa dole ne a janye karin kudin makaranta da aka yi musu sannan a bude shafin rajistar Intanet na Jami’ar da aka rufe.

Olawale ya ce babbar hanyar da suka rufe ba za su bude ta ba matukar shugaban Jami’ar Farfesa Abdul-Rasheed Na-Allah, bai saurari kokensu ba.

Da yake jawabi kan zanga-zangar, kakakin jami’ar Habib Yakoob, ya ce za su zauna da daliban a teburin sulhu don nemo mafita.
Zanga-zangar dai ta kawo tsaiko ga masu ababen hawa, da sauran jama’a da ke amfani da wannan hanya.