Dalilai 2 da suka sa Gwamna Lalong ya kai wa Buhari ziyara
Ya ce bukatar da ta dace ita ce yi wa rundunar kwaskwarima domin ingantar harkokinta na gudanarwa.
Shugaba Buhari da Gwamna Lalong
A ranar Alhamis, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Simon Bako Lalong na jihar Filato, ya ziyarci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari domin yi masa karin haske kan yanayin tsaro a yankin Arewa.
Gwamna Lalong yayin amsa tambayoyin manema labarai na fadar Shugaban Kasa, ya ce ya kuma sanar da Shugaba Buhari a kan shirin gudanar da bikin baje kolin al’adu na kasa (NAFEST) a jihar Katsina da ta kasance mahaifa ga Shugaban Kasar.
Yayin da ya ke jawabi a kan rushe rundunar tsaro ta SARS, Gwamnan ya ce bukatar da ta dace ita ce yi wa rundunar kwaskwarima domin inganta harkokinta na gudanarwa.
A cewarsa, ba dukkanin jami’an rundunar bane bara gurbi, domin kuwa ta kunshi jami’ai masu jajircewa da aiki a kan tsari kamar yadda doka ta tanada.
Ya yi gargadin cewa kada a juya wa rundunar baya domin kuwa yankin Arewacin Najeriya ya ribaci tasirinta wajen magance matsalar tsaro da ta addabi yankin.