Dalilin batawar Shata da Mammalo Shata – Sarkin Yakin Mammalo
Ga masu sauraron wakokin gargajiya na su marigayi Alhaji Mamman Shata Katsina suna sane da cewa sun yi takaddama da marigayi Alhaji Mammalo Shata. Aminiya ta yi kicibis da Alhaji Sule Sarkin Yakin Mammalo Shata wanda a gabansa aka fara rikici a tsakanin Mamman Shata da amininsa Alhaji Mammalo Shata, inda ya bayyana yadda al’amarin […]

Ga masu sauraron wakokin gargajiya na su marigayi Alhaji Mamman Shata Katsina suna sane da cewa sun yi takaddama da marigayi Alhaji Mammalo Shata. Aminiya ta yi kicibis da Alhaji Sule Sarkin Yakin Mammalo Shata wanda a gabansa aka fara rikici a tsakanin Mamman Shata da amininsa Alhaji Mammalo Shata, inda ya bayyana yadda al’amarin ya auku:
Aminiya: Mene takaitaccen tarihinka?
Sarkin Yakin Mammalo: Sunana Alhaji Sule Sarkin Yakin Mammalo Shata. Ni Baguddire ne mutumin kasar Azare ta Jihar Bauchi daga garin Gamawa, sunan kauyenmu Tarmasuwa. Roko gadon gidanmu ne. Na fito yawon duniya inda na fara haduwa da danduna Maigaraya a Bauchi, sai ya ce in raka shi Jos. Na ce a’a don ina tare da kanena marigayi Yakubu Maigoge. Sai ya ce kwanaki bakwai za mu yi mu dawo. Da muka koma Bauchi sai ya ce in raka shi Saminaka, daga nan muka wuce Gadar Gayan. To shi danduna dan caca ne, da aka cinye shi karkaf da garayar da fitilar wuta, sai ya watsar da ni ya tafi Kaduna. Sai Mamman Gadar Gayan ya dauki nauyina. Daga nan ya sa ni a motar soja mai yi wa dawaki ciyawa don in nemi danduna a wurin sukuwa a Kaduna. Sai na je Unguwar Doki inda na gan shi an cinye shi a caca ya yi zugum. Sai ya ce da wa kuka zo, sai ne ce masa kai da wa kuka zo, sai ya ce Allah Ya kawo ni. Sai na ce ni ma Shi Ya kawo ni. Sanadin zuwana Kaduna ke nan. Bayan kwana bakwai sai ya samu kudi ya ba ni ya ce in je Gadar-Gayan in karbo masa kayan kidansa, garaya da fitilar wuta. Sannan muka yi kade-kade a gidan rediyon bakin kasuwa. Sai ya ce mu je Kano, sai na ce ai na zo Kaduna ke nan. Na ce ba ka san gidanmu ko iyayena a Bauchi ba, na ce ba ni zuwa, don na iso bariki, don haka ka tafi ka bar ni a nan. Sai ya bar ni a wurin wani maroki ana ce masa dan-Musulmi a cikin Doka, Kaduna.
Aminiya: Yaya aka yi kuka hadu da mai gidanka Mammalo Shata?
Sarkin Yakin Mammalo Shata: Bayan da Mammalo Shata ya dawo daga Makka wanda ubangidansa Alhaji Ummaaru Gwagwada ya biya masa sai ya dauke ni. Kuma mun shekara 20. Sunansa na yanka Muhammadu Tasi’u. Sai aka maida shi Mammalo. Lokacin kamfen din siyasar Shagari sai Alhaji Barure Sarkin Magana ya kama hannun Shagari ya hada da na Mammalo Shata yace ka nada shi Sarkin Yakin NPN. Nana take aka dauko Babbar-Riga aka sa masa, aka ware yadi hudu aka nada masa rawani.
Aminiya: Me ya kawo batawa a tsakanin Mamman Shata da Mammalo Shata?
Sarkin Yakin Mammalo: Abin bai kai yadda mutane ke yayatawa ba. Tarihin da ya kamata a sani shi ne idan an hadu da Shata sai Mammalo da yaransa su bi Shata suna yi masa amshi. In kuma an gama kowa ya kama gabansa. Har Shata ya nada Mammalo Shata a matsayin Sarkin Yakin Mamman Shata. Idan Mamman Shata ya kafa wasa a Kaduna sai mu daina wasa har sai ya bar gari. Bayan kammala bikin nadin Alhaji Bello a matsayin Galadiman Katagum sai Mamman Shata ya koma gida mu kuma muka nufi Yola. Sai ciwon basir ya kama Mammalo Shata, muka dawo aka kwantar da shi a asibitin Jos. Sai Alhaji Ummaru Gwagwada ya maida shi Kaduna. Mammalo ya yi jinya na wata uku sannan har da karin jini, inda mu yaransa da yaran danlami Nasarawa muka bayar sannan ya warke, amma Mamman Shata bai zo ba, bai aiko ba. Bayan mako biyu da fitowarsa daga asibiti sai Alhaji Ahmadu Chanchangi ya auri ’yar gidan Sheikh Ibrahim Arab. Aka kirawo Shata daga Legas wajen Wili dan Tijjani, aka yi biki aka gama Shata bai tura a duba Mammalo ba. Sai Mammalo ya ce mu je mu duba Shata, sai na ce a’a don bai zo ba, bai aiko ba. Sai ya ce mu je mu gaishe shi. Ya dafa kafadata muka je gidan Chanchangi muka samu Chanchangi da Shata suna hira, muka gaishe su. Sai Shata ya bude baki ya ce “Warin gawa nake ji, dakin nan ya baci saboda da haka Chanchangi ka sallame ni zan tafi warin gawa ya dame ni.”
Sai Chanchangi ya tashi ya dauko kudi ya ba Shata. Shata ya ban kudin da makulli na kai masa bayan mota. Da zai tafi sai muka raka shi. Sai ya ce wa Mammalo ya shiga mota. Shata ya kai shi kusa da Rigachikun sai ya tsaya ya ce “Ga waka ka iya amma ba ka da gata, amma ba ka da ubangida mai karfi, ba ka da gida ba ka da mota, fita min a mota, ko in harbe ka.”
Mammalo ya sauka Shata ya ja mota. Yana zaune a gefen hanya sai wani ya taho daga Zariya ya ga Mammalo ya dauko shi. Mammalo da Sarkin Magana wanda shi ma a da mutumin Mamman Shata ne kafin a bata suka yi dabara sai da aka tsare Mamman Shata, sannan Mammalo ya yi wa Shata martani da wakar Gagarabadau da a ciki yake cewa:

“Ga Sarkin wakan Arewa na saida itace.
Gagarabadau namiji tsayayyen dan kasuwa.
Na yi gonar masara bakin biri zai mini barna.
Gagarabadau namiji tsayayyen dan kasuwa.
Yanzu nai mata shingen waya, biri sai dai leke.
Gagarabadau namiji tsayayyen dan kasuwa.
Aminiya: Yau shekarun Mammalo Shata nawa da rasuwa?
Sarkin Yakin Mammalo: Bayan mun dawo daga kamfen din Shugaban kasa Alhaji Shehu Shagari a Gboko da ke Jihar Benuwai da kuma nadin Sarkin Misau Alhaji Muhammadu Manga a 1983 ne, Allah Ya yi masa rasuwa.