Dalilin da ba na kewar barin kujerar shugabancin Najeriya — Buhari

Ina jin likita na ne kaɗai zai iya ba da hakikanin amsa a kan koshin lafiyata.

Dalilin da ba na kewar barin kujerar shugabancin Najeriya — Buhari

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ce kawo yanzu ko kadan ba ya kewar barin kujerar shugabancin Najeriya.

Buhari ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Gidan Talabijin na Kasa NTA.

Bayanai sun ce wannan ita ce hirarsa ta farko tun bayan kammala wa’adin mulkinsa na karshe a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Da yake amsa tambayar abin da ya fi kewa a yanzu bayan barin kujerar shugabancin Najeriya, Buhari ya ce “ba na jin akwai wani abin da nake kewa a yanzu.”

Cikin sanarwar da NTA ya wallafa a shafinsa na X, ya ce za a saki cikakkiyar hirar da aka yi da Buharin da misalin karfe 10:30 na safiyar ranar Litinin.

Tun ba yanzu ba dai Buhari ya sha cewa ba zai yi kewar barin kujerar shugabancin Najeriya ba, saboda duk abin da yake yi ba a gani.

A watan Disambar 2022 ne tsohon Shugaban Kasar ya ce yana yi wa ’yan Najeriya iyaka kokarinsa amma ba a yabawa.

Daga shekarar 2015 zuwa 2021, Buhari ya shafe kwanaki 171 a Birtaniya wajen neman lafiya, inda a shekarar 2017 kaɗai, ya shafe kwanaki 152 yana neman lafiya.

“Ina jin likita na ne kaɗai zai iya ba da hakikanin amsa a kan koshin lafiyata,” a cewar Buharin da aka tambaye shi kan rashin lafiyar da ya yi fama da ita.

Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’

Miƙa makaman ’yan bindigar Katsina ya bar baya da ƙura

Fitaccen ɗan siyasa Ahmadu Haruna Zago ya rasu

NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Ke Durƙusar Da Gidajen Rediyo A Arewa