Dalilin da ya sa na ajiye limancin masallacin Jami’ar ATBU — Farfesa Yelwa
Malamin ya ce gina sabon masallaci a jami’ar zai haddasa rarrabuwar kawuna.
Fitaccen malamin addinin Musulunci nan, Farfesa Mansur Isa Yelwa, ya bayyana dalilin da ya sa ya yi murabus daga muƙaminsa na Babban Limami kuma jagoran ayyukan wa’azin Musulunci a Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi.
Ya sanar da murabus ɗinsa ne lokacin da yake huɗuba a ranar Juma’ar da ta gabata.
- An kama ’yan uwan juna kan zargin yi wa ’yar shekara 15 fyaɗe a Delta
- Mahara sun kashe manoma 6 a kauyen Malumfashi
Farfesa Yelwa, ya bayyana cewa ya sauka ne bayan da hukumar jami’ar ta amince wa ƙungiyar ɗalibai ta ɗarikar Tijjaniyya su gina masallacinsu na musamman a cikin jami’ar.
Ya bayyana cewa jami’ar ba ta nemi shawararsa ba kafin ta yanke wannan hukunci.
Farfesan, ya ce akwai fargabar samun rabe-raben masallatai na ɓangaranci wanda zai haifar da tsaiko wajen zaman lafiya da haɗin kai a jami’ar.
Ya yi gargaɗin cewa idan har aka samar wa ɗarikar Tijjaniyya masallacinsu, to nan ba da daɗewa ba sauran ƙungiyoyin kamar Izala, Salafiyya, da Shi’a za su nemi a ba su filin don gina nasu.
Farfesa Yelwa, ya bayyana cewa ya shafe shekaru 17 yana tafiyar da masallatan jami’ar da kuma haɗa kan ƙungiyoyin Musulmi daban-daban.
Ya bayyana cewa ba zai koma kan muƙaminsa ba har sai idan hukumar jami’ar ta janye amincewar da ta bayar na gina sabon masallacin.