Dan kasuwa Femi Otedola zai yi takarar Gwamnan Jihar Legas

Dan kasuwa kuma shugaban Kamfanin Forte Oil PLC, ya amince zai iya takarar kujerar Gwamnan Jihar Legas a karkashin inuwar Jam’iyyar PDP. Dele Momudu, wanda shi ne shugaban Mujallasr Ovation ne ya sanar da hakan a shafinsa tiwita, inda ya rubuta cewa PDP ce ta yi wa Otedola tayi, kuma ya amsa. “Zaben Gwamnan Jihar […]

Dan kasuwa Femi Otedola zai yi takarar Gwamnan Jihar Legas
Dan kasuwa Femi Otedola zai yi takarar Gwamnan Jihar Legas

Dan kasuwa kuma shugaban Kamfanin Forte Oil PLC, ya amince zai iya takarar kujerar Gwamnan Jihar Legas a karkashin inuwar Jam’iyyar PDP.

Dele Momudu, wanda shi ne shugaban Mujallasr Ovation ne ya sanar da hakan a shafinsa tiwita, inda ya rubuta cewa PDP ce ta yi wa Otedola tayi, kuma ya amsa.

“Zaben Gwamnan Jihar Legas a shekarar 2019 zai yi armashi. Jam’iyyar PDP ta yi wa Femi Otedola tayin tikitin takara, kuma ya tabbatar mana wa shugaban Jaridar Boss cewa ya amince.”

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa