Dan kwamitin amintatttun PDP ya bar jam’iyyar

Farfesa Alphonsus Nwosu, na hannun daman Atiku ya fice daga PDP

Dan kwamitin amintatttun PDP ya bar jam’iyyar

Mamba a Kwamitin Amintatttun Jam’iyyar PDP, Farfesa Alphonsus Nwosu, ya fice daga jam’iyyar.

Farfesa Alphonsus Nwosu tsohon Ministan Lafiya ne kuma na hannun daman dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Ya bayyana rashin bin tsarin karba-karbar takarar shugaban kasa a PDP a matsayin dalilinsa na raba gari da ficewarsa ita.

Tuni dai ya aike wa Shugaba PDP na Ƙasa, Iyorchia Ayu da Shugaban Riko na Kwamitin Amintatttun jam’iyyar, Adolphus Wabara da kuma shugaban mazabarsa takardarsa ta ficewa daga jam’iyyar.

Farfesa Nwosu na daga cikin iyayen PDP da aka kafa a ta da su.

Ya kuma taka muhimmiyar rawa a mukaman jam’iyyar da ya rike a matakin kasa da kuma yankin Kudu.

An kama mutum uku da ƙwato wayoyin lantarki na sata 

Zan ci gaba da bada kuɗin hadaya kyauta — Gwamna Zulum 

Obasanjo na yunƙurin ɓata min suna don ɗan takararsa — Atiku

Sojoji sun kama masu garkuwa da mutane a Yobe