Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya suya sheka daga PDP zuwa APC

Ya ce kafin ya sauya shekar sai da ya tuntubi al’ummar mazabarsa inda suka ba shi hadin kai da kuma amincewa.

Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya suya sheka daga PDP zuwa APC

Dan Majalisar Tarayya mai Wakiltar Zangon Kataf/Jaba daga Jihar Kaduna, Honorabul Amos Gwamna Magaji ya sauya sheka daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki.

A safiyar Talata Shugaban Majalisar, Abbas Tajuddeen ya sanar da sauya shekar, yana mai bayyana rikicin cikin gidan PDP a mastayin dalilin ficewar dan majalisar daga jam’iyyar.

Dan majalisar ya  bayyana cewa kafin ya sauya shekar sai da ya tuntubi al’ummar mazabarsa inda suka ba shi hadin kai da kuma amincewa.

Sai dai Shugaban Marasa Rinjaye, Kingsley Chinda (PDP) ya daga kara da cewa ko da yake dan majalisar na da hurumin sauya sheka, amm ya kamata a bi abin da doka ta tanada.

Honorabul Chinda ya bayyana cewa daga cikin abubuwan da doka ta tanada akwai yiwuwar kwace kujerar dan majalisar da ya sauya sheka, idan bai cika ka’idojin da suka dace ba.
Amma shugaban majalisar ya bayyana cewa dan majalisar ya riga ya ba da dalilinsa na sauya sheka, kuma ya dace da abin da doka ta tanada.

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’

BUA ya raba wa asibitoci magunguna a Sakkwato

Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya suya sheka daga PDP zuwa APC