Dan Majalisar Wakilai na Karamar Hukumar Bakori ya rasu a Saudiyya
Ya rasu a birnin Madinah.
Dan Majalisar Wakilai na Karamar Hukumar Bakori ta Jihar Katsina, Honorabul Dokta Ibrahim Aminu Kurami
Dan Majalisar Wakilai na Karamar Hukumar Bakori ta Jihar Katsina, Honorabul Dokta Ibrahim Aminu Kurami ya rasu a Saudiyya.
Hon. Dokta Ibrahim Aminu Kurami ya rasu ne a kasa mai tsarki yayin da ya je aikin umara.
- An sace kanwar Mataimakin Shugaban Majalisar Katsina
- Gobarar kwale-kwale ta hallaka ‘yan ci rani a tsakiyar Teku
Dan Majalisar ya rasu ne bayan ’yar gajeruwar rashin lafiya da ya yi a birnin Madina da misalin karfe 2:00 na daren Litinin din nan.
Idan ba ku manta. ba an yi zabi Dan Majalisar ne a shekarar 2020 bayan rasuwar tsohon dan majalisar Honorabul Abdurrazak Ismail Tsiga a zaben cike gurbi da aka gudanar a jihar.