Dan uwan Sarkin Musulmi ya rasu

Wan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya rasu

Dan uwan Sarkin Musulmi ya rasu

Allah Ya yi wa yayan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III rasuwa.

Alhaji Buhari Abubakar III ya rasu ne ranar Juma’a a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, bayan fama da rashin lafiya.

Kafin rasuwarsa, Alhaji Buhari Abubakar III shi ne Hakimin Sakkwato ta Arewa.

Rasuwar tasa ita ce babba ta biyu da aka yi a gidan sarautar Masarautar Daular Usmaniyya a rana guda.

Tun da farko Aminiya ta kawo rahoton rasuwar ’yar Sardaunan Sakkwato, Alhaji Ahmadu Bello, mai suna Aisha.

Sardauna Ahmadu Bello, jika ne ga Sarki Muhammadu Bello, wanda da ne ga Shehu Usmanu Danfodiyo, wanda ya assasa Daular ta Usmaniyya.

Hajiya A’i, kamar yadda aka fi sanin ta, ta rasu tana da shekara 76, a asibiti a birnin Dubai na Haddaddiyar Daular Larabawa, inda aka yi  jinyar ta, Hassan Dambaba, ya sanar.

Marigayiyar, ita ce ta biyu a cikin ’ya’yan marigayi Sardauna, kuma mata  ce ga marigayi Marafan Sakkwato, Alhaji Ahmad Danbaba.

Na ƙi biyan kuɗin fansar ’yan uwana sun kuɓuta — Gwamnan Zamfara

Ma’aikatan Abuja ba sa sona — Wike

Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Gwamnati ta ƙara albashin sojoji — Ministan Tsaro