Dikko Radda ya jagoranci taro kan matsalar ’yan daba a Katsina

aron ya haɗa jami’an tsaro, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki, inda aka mayar da hankali kan yawaitar rikice-rikicen ’yan daba da faɗace-faɗace tsakanin kungiyoyin matasa a cikin birnin Katsina

Dikko Radda ya jagoranci taro kan matsalar ’yan daba a Katsina

‘Yan daba

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya gudanar da muhimmin taron tsaro tare da manyan wakilai daga Karamar Hukumar Katsina domin tattauna matsalar tsaro da ke ƙara taɓarɓarewa a yankin.

Taron ya haɗa jami’an tsaro, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki, inda aka mayar da hankali kan yawaitar rikice-rikicen ’yan daba da faɗace-faɗace tsakanin kungiyoyin matasa a cikin birnin Katsina.

Wakilan karamar hukumar, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar Katsina, Hon. Isah Miqdad, sun tattauna da gwamna kan hanyoyin da za su kawo ƙarshen barazanar tsaro da ke tasowa.

A yayin tattaunawar, mahalarta taron sun yi cikakken nazari kan halin tsaro a yankin, tare da gano manyan dalilan rikice-rikicen da kuma gabatar da shawarwari na zahiri domin ƙarfafa tsaro da dawo da kwarin gwiwar jama’a.

Gwamna Radda ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na yaki da matsalar tsaro, inda ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga hukumomin kananan hukumomi.

Ya kuma jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, shugabannin al’umma da mazauna yankin wajen dakile matsalar.

A cikin mahalarta taron akwai Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Ƙasa, Nasiru Mu’azu; Kwamishinan Shari’a, Barista Fadila Mohammed Dikko; da ɗan majalisar da ke wakiltar yankin, Aliyu Abubakar Albaba.

Haka kuma, Kwamishinan ’yan sanda, shugabannin sauran hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya, shugabannin addini da wakilan ’yan kasuwa sun halarta.

A tun farko cikin watan nan, Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta yi kira kan ƙara yawaitar matsalar ’yan daba a cikin birnin, inda ta aika da damuwarta ga bangaren zartarwa domin daukar mataki.

An gano baƙin haure 30 a ɓoye cikin tankar mai a Turkiyya

An tsare ɗan gwagwarmaya kan sukar gwamnatin sojin Nijar

Alhazan Kebbi rukunin farko sun dawo gida

Rukunin farko na Alhazan Kebbi 426 sun dawo gida