Direba ya kashe matarsa da `ya `yansa 2 a Edo
Hukumar `yan sandan jihar Edo ta tsare wani direba mai suna Uwaila Idehen dan shekara 35 akan tuhumarsa da laifin kashe matarsa da kuma `ya `yansu biyu. Kwamishinan `yan sandan jihar Edo Hakeem Olusegun Odumosu ya ce, Uwaila na daya daga cikin mutum 110 da ake zarginsu da aikata laifuka a jihar da aka gurfanar […]
Hukumar `yan sandan jihar Edo ta tsare wani direba mai suna Uwaila Idehen dan shekara 35 akan tuhumarsa da laifin kashe matarsa da kuma `ya `yansu biyu.
Kwamishinan `yan sandan jihar Edo Hakeem Olusegun Odumosu ya ce, Uwaila na daya daga cikin mutum 110 da ake zarginsu da aikata laifuka a jihar da aka gurfanar da su.
Kwamishinan ya ce, wadanda ake zargin an tsare su ne akan wasu laifuka da suka hada da: tsafi da fashi da makami, yin garkuwa da mutane, sace-sace da kuma aikata fyade.